• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya Ta Mulkin Tinubu: Nijeriya Ta Fara Ganin Sauyi Wajen Samun Kwanciyar Hankali Da Arziki Da Tsaro – Minista

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
Shekara Ɗaya Ta Mulkin Tinubu: Nijeriya Ta Fara Ganin Sauyi Wajen Samun Kwanciyar Hankali Da Arziki Da Tsaro – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Nijeriya ta fara tafiya mai kawo sauyi ta fuskar samun kwanciyar hankali da arziki da tsaro, wanda Ajandar Sabunta Fata Mai Lamba 8 ta ƙunsa a cikin shekara ta farko tun bayan hawan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ministan ya bayyana haka ne a cikin wani rahoto da ma’aikatar sa ta fitar a ranar Talata mai taken “Shekara Ɗaya ta Gwamnatin Tinubu – Gina Nijeriya mai Tsaro, Ƙarfi, da Wadata,” wanda ke bayyana gagarumin cigaban da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubu, na tunkarar manyan matsalolin ƙasa da aiwatar da ingantattun manufofi da nufin samar da haɓaka da cigaban ƙasa.

  • Ina Kokarin Cika Alkawuran Da Na Dauka – Tinubu 
  •  ‘Yancin Taiwan Na Nufin Yaki, In Ji Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin

Rahoton ya ce, “A yayin da ake fama da matsalolin tattalin arziki da tashe-tashen hankula da rashin aikin yi suka haifar, sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnati ta yi sun daidaita tattalin arzikin ƙasar tare da haifar da cigaba.

“Wani muhimmin yunƙuri shi ne kawar da tallafin man fetur maras ɗorewa, da karkatar da kusan dala biliyan 10 kowace shekara zuwa sassa masu muhimmanci kamar kiwon lafiya, ilimi, ababen more rayuwa, da tsaro.

“Wannan mataki kaɗai ya haifar da raguwar shigo da mai da kashi 50 cikin 100 tare da ƙaruwar kuɗaɗen shiga na jihohi da ƙananan hukumomi. Kawar da tallafin kuɗin ƙasashen waje da kuma daidaita farashin canji ya ƙarfafa tattalin arzikin Nijeriya, wanda hakan ya sanya Kasuwar Hada-hadar Hannun Jari ta Nijeriya ta zama kan gaba a kasuwannin duniya tare da ƙarfafa darajar Naira.”

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Rahoton ya ƙara da cewa, “Domin samun sauƙin tasirin waɗannan matakan tattalin arziki, gwamnatin ta ƙaddamar da wasu ayyuka da suka haɗa da biyan albashin naira 35,000 ga ma’aikatan gwamnati duk wata, kafa kwamitin sake fasalin albashi, da kuma samar da Asusun Tallafa wa Jihohi.

“Ɓangaren ƙasa da ƙasa, gwamnatin ta samu nasarar jawo jarin sama da dala biliyan 30, wanda hakan ya ƙara haɓaka tattalin arzikin Nijeriya.

“Tsaro ya kasance babban abin da aka fi mayar da hankali a kan shi, tare da zuba jari mai yawa da nufin zamanintar da rundunonin sojoji da kuma cimma muhimman nasarori a harkar tsaron ƙasa.

“Wannan yunƙurin ya haifar da ‘yantar da mutane sama da 4,600 da aka yi garkuwa da su, tare da kawar da masu laifi 9,300, tare da kama ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga 7,000.

“Jami’an tsaron sun kuma ƙwato dubban makamai da harsasai, wanda hakan na da muhimmanci wajen yaƙar ‘yan fashi da masu tayar da ƙayar baya.

A yayin da yake tunkarar matsalar samar da abinci, Shugaba Tinubu ya kafa dokar ta-ɓaci, wanda ya kai ga sake fasalin Ma’aikatar Noma zuwa Ma’aikatar Noma da Samar da Abinci.

An ƙaddamar da shirye-shirye irin su Asusun Bunƙasa Noma na Ƙasa da Shirin Noman Rani don bunƙasa aikin noma da tabbatar da wadatar abinci.

“An inganta matakan tsaro wajen kula da makamashi da albarkatun ƙasa a yankin Neja Delta, lamarin da ya haifar da ƙaruwar haƙo mai da ƙarin iskar gas. Haka kuma an ba da fifiko wajen samar da ababen more rayuwa, tare da zuba jari mai yawa a hanyoyin sufuri da suka haɗa da ƙaddamar da sabbin layukan dogo da ƙaddamar da babban titin Legas zuwa Kalaba, da ƙaddamar da Tsarin Babbar Hanyar Sokoto zuwa Badagry.

“An haɓaka fannin kiwon lafiya da ilimi sosai a ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata. Faɗaɗa cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko da gabatar da dokar ba da lamuni ga ɗalibai (Samun Ilimi Mai Girma) wani ɓangare ne na ƙoƙarin inganta hanyoyin samun muhimman ayyuka da damarmaki ga dukkan ‘yan Nijeriya.

“A yayin da muke ci gaba da tafiya, gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da jajircewa wajen ganin ta na tabbatar da Nijeriya mai ɗorewa da wadatar arziki, wadda za ta kasance ƙarƙashin zuba jari, da ƙarfafa matasa, da inganta harkokin mulki.

“Cigaban da aka samu a cikin shekara guda kacal ya kafa ginshiƙin haɓaka da cigaba mai ɗorewa, tare da yin alƙawarin samun kyakkyawar rayuwa a nan gaba ga dukkan ‘yan Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan NijeriyaGwamnatin TinubuMinistan Yaɗa Labarai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hakkin Bil Adam Iri Na Amurka Matakin Gatanci Da Babakere Ne

Next Post

Xi Jinping: Sin Na Fatan Kafa Tsare-Tsaren Hadin Kai Biyar Tsakaninta Da Kasashen Larabawa

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

4 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

7 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

8 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

10 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

11 hours ago
Next Post
Xi Jinping: Sin Na Fatan Kafa Tsare-Tsaren Hadin Kai Biyar Tsakaninta Da Kasashen Larabawa

Xi Jinping: Sin Na Fatan Kafa Tsare-Tsaren Hadin Kai Biyar Tsakaninta Da Kasashen Larabawa

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.