ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya Ta Mulkin Tinubu: Nijeriya Ta Fara Ganin Sauyi Wajen Samun Kwanciyar Hankali Da Arziki Da Tsaro – Minista

by Sulaiman
2 years ago
Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Nijeriya ta fara tafiya mai kawo sauyi ta fuskar samun kwanciyar hankali da arziki da tsaro, wanda Ajandar Sabunta Fata Mai Lamba 8 ta ƙunsa a cikin shekara ta farko tun bayan hawan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan karagar mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Ministan ya bayyana haka ne a cikin wani rahoto da ma’aikatar sa ta fitar a ranar Talata mai taken “Shekara Ɗaya ta Gwamnatin Tinubu – Gina Nijeriya mai Tsaro, Ƙarfi, da Wadata,” wanda ke bayyana gagarumin cigaban da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Tinubu, na tunkarar manyan matsalolin ƙasa da aiwatar da ingantattun manufofi da nufin samar da haɓaka da cigaban ƙasa.

  • Ina Kokarin Cika Alkawuran Da Na Dauka – Tinubu 
  •  ‘Yancin Taiwan Na Nufin Yaki, In Ji Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin

Rahoton ya ce, “A yayin da ake fama da matsalolin tattalin arziki da tashe-tashen hankula da rashin aikin yi suka haifar, sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnati ta yi sun daidaita tattalin arzikin ƙasar tare da haifar da cigaba.

ADVERTISEMENT

“Wani muhimmin yunƙuri shi ne kawar da tallafin man fetur maras ɗorewa, da karkatar da kusan dala biliyan 10 kowace shekara zuwa sassa masu muhimmanci kamar kiwon lafiya, ilimi, ababen more rayuwa, da tsaro.

“Wannan mataki kaɗai ya haifar da raguwar shigo da mai da kashi 50 cikin 100 tare da ƙaruwar kuɗaɗen shiga na jihohi da ƙananan hukumomi. Kawar da tallafin kuɗin ƙasashen waje da kuma daidaita farashin canji ya ƙarfafa tattalin arzikin Nijeriya, wanda hakan ya sanya Kasuwar Hada-hadar Hannun Jari ta Nijeriya ta zama kan gaba a kasuwannin duniya tare da ƙarfafa darajar Naira.”

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Rahoton ya ƙara da cewa, “Domin samun sauƙin tasirin waɗannan matakan tattalin arziki, gwamnatin ta ƙaddamar da wasu ayyuka da suka haɗa da biyan albashin naira 35,000 ga ma’aikatan gwamnati duk wata, kafa kwamitin sake fasalin albashi, da kuma samar da Asusun Tallafa wa Jihohi.

“Ɓangaren ƙasa da ƙasa, gwamnatin ta samu nasarar jawo jarin sama da dala biliyan 30, wanda hakan ya ƙara haɓaka tattalin arzikin Nijeriya.

“Tsaro ya kasance babban abin da aka fi mayar da hankali a kan shi, tare da zuba jari mai yawa da nufin zamanintar da rundunonin sojoji da kuma cimma muhimman nasarori a harkar tsaron ƙasa.

“Wannan yunƙurin ya haifar da ‘yantar da mutane sama da 4,600 da aka yi garkuwa da su, tare da kawar da masu laifi 9,300, tare da kama ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga 7,000.

“Jami’an tsaron sun kuma ƙwato dubban makamai da harsasai, wanda hakan na da muhimmanci wajen yaƙar ‘yan fashi da masu tayar da ƙayar baya.

A yayin da yake tunkarar matsalar samar da abinci, Shugaba Tinubu ya kafa dokar ta-ɓaci, wanda ya kai ga sake fasalin Ma’aikatar Noma zuwa Ma’aikatar Noma da Samar da Abinci.

An ƙaddamar da shirye-shirye irin su Asusun Bunƙasa Noma na Ƙasa da Shirin Noman Rani don bunƙasa aikin noma da tabbatar da wadatar abinci.

“An inganta matakan tsaro wajen kula da makamashi da albarkatun ƙasa a yankin Neja Delta, lamarin da ya haifar da ƙaruwar haƙo mai da ƙarin iskar gas. Haka kuma an ba da fifiko wajen samar da ababen more rayuwa, tare da zuba jari mai yawa a hanyoyin sufuri da suka haɗa da ƙaddamar da sabbin layukan dogo da ƙaddamar da babban titin Legas zuwa Kalaba, da ƙaddamar da Tsarin Babbar Hanyar Sokoto zuwa Badagry.

“An haɓaka fannin kiwon lafiya da ilimi sosai a ƙarƙashin Ajandar Sabunta Fata. Faɗaɗa cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko da gabatar da dokar ba da lamuni ga ɗalibai (Samun Ilimi Mai Girma) wani ɓangare ne na ƙoƙarin inganta hanyoyin samun muhimman ayyuka da damarmaki ga dukkan ‘yan Nijeriya.

“A yayin da muke ci gaba da tafiya, gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da jajircewa wajen ganin ta na tabbatar da Nijeriya mai ɗorewa da wadatar arziki, wadda za ta kasance ƙarƙashin zuba jari, da ƙarfafa matasa, da inganta harkokin mulki.

“Cigaban da aka samu a cikin shekara guda kacal ya kafa ginshiƙin haɓaka da cigaba mai ɗorewa, tare da yin alƙawarin samun kyakkyawar rayuwa a nan gaba ga dukkan ‘yan Nijeriya.”

Tinubu
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Xi Jinping: Sin Na Fatan Kafa Tsare-Tsaren Hadin Kai Biyar Tsakaninta Da Kasashen Larabawa

Xi Jinping: Sin Na Fatan Kafa Tsare-Tsaren Hadin Kai Biyar Tsakaninta Da Kasashen Larabawa

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.