• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya A Mulki: Ayyukan Ci Gaban Da Muke Yi Na Samun Tagomashi A Zamfara – Gwamna Lawal

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Shekara Ɗaya A Mulki: Ayyukan Ci Gaban Da Muke Yi Na Samun Tagomashi A Zamfara – Gwamna Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada cewa ayyukan samar wa al’umma mafita da gwamnatinsa ke yi na samun tagomashi sosai, kuma an samu gagarumin sakamako cikin shekara guda.

Gwamnan ya ƙaddamar da manyan ayyuka a Ƙananan Hukumomi takwas, wanda aka fara a Ƙaramar Hukumar Gummi a ranar Lahadi, 27 ga watan Mayu.

A wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu a Gusau ranar Alhamis ɗin nan, ya bayyana cewa an ƙaddamar da wasu ayyuka huɗu a babban birnin jihar, Gusau da Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda.

Sanarwar ta ce, gwamnatin Dauda Lawal ta ƙaddamar da ɗaya daga cikin ayyukan tituna a Gusau: gyaran sakatariyar J.B. Yakubu ta jihar da kuma makarantar Tsangaya ta zamani da ke Ƙananan Hukumomin Gusau da Ƙauran Namoda.

“A ranar Talata, 28 ga watan Mayu, Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da babbar hanyar da ta haɗa shataletalen UBA zuwa Freedom Square da ke ƙwaryar garin Gusau, babban birnin jihar Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

zamfara

“Hanyar wani ɓangare ne na aikin sabunta biranen da gwamnatin ke ci gaba da yi, kuma Ambasada Umar Iliya Damagum, muƙaddashin shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa ne ya ƙaddamar da shi.

A ranar Talata, 28 ga watan Mayu ne Gwamna Lawal ya ƙaddamar da Makarantar Tsangaya ta zamani a Ƙauran Namoda.

“Makarantar Tsangaya da ke Kauran Namoda ce za ta ɗauki nauyin kula da yankin Zamfara ta Arewa, bayan kwana biyu da ƙaddamar da wata a Gummi, da nufin yi wa al’ummar mazaɓar Zamfara ta Yamma hidima. Makarantar Tsangaya ta uku kuma tana Gusau ne a gundumomin Zamfara ta tsakiya.”

A jiya, 29 ga watan Mayu, Gwamna Lawal ya ƙaddamar da wani muhimmin aiki, ginin Sakatariyar J. B. Yakubu, wadda ita ce babbar sakatariyar gwamnatin jihar Zamfara.

Da yake gabatar da jawabinsa a wajen bikin ranar 29 ga watan Mayu, Gwamna Lawal ya jaddada cewa a cikin watanni 12 da suka gabata gwamnatinsa ta samu ci gaba sosai. “Mun hada ƙarfi da ƙarfe wajen yaƙi da ’yan bindiga da sauran laifuka, mun yi gyara a sassa masu muhimmanci na ilimi, kiwon lafiya, da noma, mun ƙaddamar da ayyukan sabunta birane, da gyara tsarin ma’aikatun gwamnati, da inganta hanyoyin samun kuɗaɗen shiga a jihar, da kuma samar da ingantaccen tsarin gudanarwa a ma’aikatun gwamnati”.

A lokacin da yake ƙaddamar da Makarantar Tsangaya ta zamani da ke Gusau, Gwamna Lawal ya ƙara jaddada cewa, makarantun Tsangaya da aka sabunta, an tsara ta ne domin haɗa abubuwan da suka shafi ilimin zamani na Boko da koyarwar addinin Musulunci a lokaci guda.

“Kamar yadda na ambata a Gummi da Ƙaura Namoda, tsarin karatun Tsangaya ta kasance wani ɓangare na al’adunmu shekaru aru-aru. Ta kasance tushen ilimi da tarbiyya a cikin al’ummomin Musulmi a arewacin Nijeriya. Kusan kowane yaro ɗan Musulmi da ya girma a wannan yanki ya sami irin wannan nau’in ilimi.

“Wannan shiri zai taimaka matuƙa wajen rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, ƙalubalen da jihar Zamfara ta samu matsayi mafi girma. Ta hanyar buɗe wa waɗannan yara sabbin damarmaki, muna fatan za mu zaburarwa da yawa daga cikinsu da ƙwarin gwiwar ci gaba da neman ilimi a nan gaba, ta yadda za su inganta rayuwarsu da kuma bayar da gudunmawar ci gaban jiharmu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AyyukaCi GabaDauda LawalGwamnaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron Ministoci Karo Na 10 Na Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Kasar Sin Da Kasashen Larabawa Ya Zartas Da Wasu Takardun Sakamako

Next Post

Sarki Sanusi Ya Naɗa Dagacin Janguza Duk Da Rikicin Masarautar Kano

Related

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

6 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

8 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

11 hours ago
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato
Manyan Labarai

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

12 hours ago
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa
Labarai

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

13 hours ago
DSS
Labarai

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

15 hours ago
Next Post
Sanusi

Sarki Sanusi Ya Naɗa Dagacin Janguza Duk Da Rikicin Masarautar Kano

LABARAI MASU NASABA

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

Zaman Lafiya A Duniya: Mu Baje Sin Da Amurka A Faifai

June 4, 2025
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Belarus

June 4, 2025
Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.