• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya A Mulki: Ayyukan Ci Gaban Da Muke Yi Na Samun Tagomashi A Zamfara – Gwamna Lawal

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Shekara Ɗaya A Mulki: Ayyukan Ci Gaban Da Muke Yi Na Samun Tagomashi A Zamfara – Gwamna Lawal
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada cewa ayyukan samar wa al’umma mafita da gwamnatinsa ke yi na samun tagomashi sosai, kuma an samu gagarumin sakamako cikin shekara guda.

Gwamnan ya ƙaddamar da manyan ayyuka a Ƙananan Hukumomi takwas, wanda aka fara a Ƙaramar Hukumar Gummi a ranar Lahadi, 27 ga watan Mayu.

A wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya sanya wa hannu a Gusau ranar Alhamis ɗin nan, ya bayyana cewa an ƙaddamar da wasu ayyuka huɗu a babban birnin jihar, Gusau da Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda.

Sanarwar ta ce, gwamnatin Dauda Lawal ta ƙaddamar da ɗaya daga cikin ayyukan tituna a Gusau: gyaran sakatariyar J.B. Yakubu ta jihar da kuma makarantar Tsangaya ta zamani da ke Ƙananan Hukumomin Gusau da Ƙauran Namoda.

“A ranar Talata, 28 ga watan Mayu, Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da babbar hanyar da ta haɗa shataletalen UBA zuwa Freedom Square da ke ƙwaryar garin Gusau, babban birnin jihar Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

zamfara

“Hanyar wani ɓangare ne na aikin sabunta biranen da gwamnatin ke ci gaba da yi, kuma Ambasada Umar Iliya Damagum, muƙaddashin shugaban jam’iyyar PDP na ƙasa ne ya ƙaddamar da shi.

A ranar Talata, 28 ga watan Mayu ne Gwamna Lawal ya ƙaddamar da Makarantar Tsangaya ta zamani a Ƙauran Namoda.

“Makarantar Tsangaya da ke Kauran Namoda ce za ta ɗauki nauyin kula da yankin Zamfara ta Arewa, bayan kwana biyu da ƙaddamar da wata a Gummi, da nufin yi wa al’ummar mazaɓar Zamfara ta Yamma hidima. Makarantar Tsangaya ta uku kuma tana Gusau ne a gundumomin Zamfara ta tsakiya.”

A jiya, 29 ga watan Mayu, Gwamna Lawal ya ƙaddamar da wani muhimmin aiki, ginin Sakatariyar J. B. Yakubu, wadda ita ce babbar sakatariyar gwamnatin jihar Zamfara.

Da yake gabatar da jawabinsa a wajen bikin ranar 29 ga watan Mayu, Gwamna Lawal ya jaddada cewa a cikin watanni 12 da suka gabata gwamnatinsa ta samu ci gaba sosai. “Mun hada ƙarfi da ƙarfe wajen yaƙi da ’yan bindiga da sauran laifuka, mun yi gyara a sassa masu muhimmanci na ilimi, kiwon lafiya, da noma, mun ƙaddamar da ayyukan sabunta birane, da gyara tsarin ma’aikatun gwamnati, da inganta hanyoyin samun kuɗaɗen shiga a jihar, da kuma samar da ingantaccen tsarin gudanarwa a ma’aikatun gwamnati”.

A lokacin da yake ƙaddamar da Makarantar Tsangaya ta zamani da ke Gusau, Gwamna Lawal ya ƙara jaddada cewa, makarantun Tsangaya da aka sabunta, an tsara ta ne domin haɗa abubuwan da suka shafi ilimin zamani na Boko da koyarwar addinin Musulunci a lokaci guda.

“Kamar yadda na ambata a Gummi da Ƙaura Namoda, tsarin karatun Tsangaya ta kasance wani ɓangare na al’adunmu shekaru aru-aru. Ta kasance tushen ilimi da tarbiyya a cikin al’ummomin Musulmi a arewacin Nijeriya. Kusan kowane yaro ɗan Musulmi da ya girma a wannan yanki ya sami irin wannan nau’in ilimi.

“Wannan shiri zai taimaka matuƙa wajen rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta, ƙalubalen da jihar Zamfara ta samu matsayi mafi girma. Ta hanyar buɗe wa waɗannan yara sabbin damarmaki, muna fatan za mu zaburarwa da yawa daga cikinsu da ƙwarin gwiwar ci gaba da neman ilimi a nan gaba, ta yadda za su inganta rayuwarsu da kuma bayar da gudunmawar ci gaban jiharmu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AyyukaCi GabaDauda LawalGwamnaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron Ministoci Karo Na 10 Na Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Kasar Sin Da Kasashen Larabawa Ya Zartas Da Wasu Takardun Sakamako

Next Post

Sarki Sanusi Ya Naɗa Dagacin Janguza Duk Da Rikicin Masarautar Kano

Related

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

4 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

9 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

10 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

11 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

13 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

16 hours ago
Next Post
Sanusi

Sarki Sanusi Ya Naɗa Dagacin Janguza Duk Da Rikicin Masarautar Kano

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.