• English
  • Business News
Sunday, June 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Ƙananan Hukumomin Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Ƙananan Hukumomin Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka a Ƙananan Hukumomin Gummi, Bukkuyum da Maru.

Gwamnatin jihar ta zayyana jerin ayyuka da aka fi sani da ‘Ayyukan Ceto Zamfara’ don tunawa da shekara ɗaya na gwamnatin Dauda Lawal a kan mulki.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta jaddada cewa an fara ƙaddamar da ayyukan ne da makarantar Tsangaya ta zamani da ke Ƙaramar Hukumar Gummi.

gwamna

A cewarsa, an sanya wa makarantar Tsangayar sunan Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III OFR, wanda ya kasance babban baƙo na musamman a wajen buɗe makarantar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

Sanarwar ta ƙara da cewa: “A yau ne gwamna Dauda Lawal ya fara rangaɗi a faɗin ƙananan hukumomin Zamfara 14 domin ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka da gwamnatinsa ta ƙaddamar a shekarar da ta gabata.

“Ayyukan an sanya su a matsayin ayyukan ceto, waɗanda suka mai da hankali kan wuraren da ke ƙara darajar rayuwar al’umma, ciki har da tsaro, kiwon lafiya, ilimi, da kayayyakin more rayuwa da sauransu.”

gwamna

Da yake gabatar da jawabinsa a ƙaramar hukumar Gummi, Gwamna Lawal ya jaddada cewa makarantar Tsangaya aiki ne da gwamnatinsa ta tsara kuma ta aiwatar a wani shiri na tabbatar da ilimin bai ɗaya ga dukkan yaran da suka isa zuwa makaranta a faɗin jihar.

“Tsarin ilimin Tsangaya ingantaccen tsarin ilimi ne a wannan yanki. Tsari ne da ake isar da tarbiyyar addini da kyawawan ɗabi’u ga duk wanda da ke cikinsa.

“Idan aka yi la’akari da muhimmancin tsarin ilimin Tsangaya ga al’ummarmu, za a ga cewa tsarin ya ƙunshi ilimin addinin Musulunci, wanda shi ne abin da Tsangaya ya mayar da hankali a kai, wanda kuma zai tafi daidai da ilimin zamani. Wannan yana nufin baiwa yaranmu ilimi da ƙwarewa don taimaka musu sanin yadda tsarin duniya ke tafiya a zamanance. Haɗa duka tsarin biyu, ita ce hanya mafi inganci ta kawo ƙarin ci gaba ga jama’armu da al’ummominmu.

gwamna

“Saboda haka tsarin zai haɗe karatun Islamiyya da ilimin zamani. Gwamnati kuma ta shigar da shi cikin Shirin Ilimi Na Kowa a jihar.

“Za a koyar da darussa kamar Ingilishi, Lissafi, Ilimin zamantakewa, da koyar da sana’o’i tare da ilimin addinin Islama, tare da haɓaka ƙwarewar yara da jin daɗin rayuwa.

“Wannan aikin ya ƙunshi gina ɗakunan kwanan ɗalibai guda tara, gidajen kwanan malamai, katangar za ta kewaye makaratar, wutar lantarki mai amfani da hasken rana, rijiyoyin burtsatse, kujeru da tebura, wuraren koyarwa da koyo da dai sauransu.

gwamna

“Bugu da ƙari, makarantar tana da cibiyar koyar da sana’o’i inda za a ba da horo a kan aikin kafinta, aikin katako, ɗinki, koyon aiki da kwamfuta da dai sauran su. Hakan zai ba su damar yin amfani da dabarun da suka samu tare da taimaka musu wajen samun abin dogaro da kai.”

A Nasarawa Burkullu, ƙaramar hukumar Bukkuyum, Gwamna Lawal ya ƙaddamar da babban asibitin da aka inganta daga cibiyar kula da lafiya ta matakin farko.

“Sabuwar ginin da aka inganta za ta samar da cikakkiyar aiki na kiwon lafiya kamar kulawar gaggawa, tiyata, kula da lafiyar mata da yara.

“Ayyukan da aka aiwatar sun haɗa da gina ƙarin gine-gine da kuma gyara waɗanda ake da su, kamar sashen keɓe masu lalura ta daman, wurin ajiyar gawa, sashen kula haɗari, ɗakin tiyata, ɗakunan tiyatar maza da mata, GOPD, ɗakin gwaje-gwaje, sashen magani, kula da mata masu juna biyu, da sashen kula da yara. Sauran sun haɗa da ɓangaren masu kula da asibiti, wuraren ma’aikata, masallatai, da rijiyoyin burtsatse.

A Ƙaramar Hukumar Maru, Gwamna Lawal ya tantance aikin gyaran babban asibitin Maru, wanda ya haɗa da gyaran dukkan gine-gine da samar da kayan aiki na zamani don bunƙasa ƙarfinta na samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AyyukaCi GabaGwamna Dauda LawalJihar ZamfaraShekara DayaTsaroZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zanga-Zanga Bayan Cire Sarki Aminu Ado, Abin Da Ya Kamata Ku Sani

Next Post

Ba Mu Jibge Dakarunmu Don Mayar Da Sarki Aminu Sarauta Ba – Sojoji

Related

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

51 minutes ago
bakin wake
Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

3 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar
Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

5 hours ago
Gwamnan kano
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

7 hours ago
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina
Labarai

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

7 hours ago
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya
Labarai

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

8 hours ago
Next Post
Rundunar Sojoji Ta Karrama Jami’anta 10 Bisa Ƙwarewa A Yaƙi Da Ta’addanci

Ba Mu Jibge Dakarunmu Don Mayar Da Sarki Aminu Sarauta Ba - Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

Binciken CGTN Ya Nuna Kaso Kusan 90 Bisa Dari Na Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kokawa Da Makomar “Mafarkin Amurka”

June 1, 2025
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah

June 1, 2025
bakin wake

Bam Ya Kashe Mutane 9 A Wata Tashar Motoci Da Ke Borno 

June 1, 2025
‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

‘Yan Wasan Da Tauraruwar Ronaldo Da Messi Ta Hana Su Haskawa

June 1, 2025
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

June 1, 2025
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

June 1, 2025
Gwamnan kano

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

June 1, 2025
Gwamna Dikko Zai Sake Tsarin Babbar Kasuwar Jihar Katsina

Majalisar Dokokin Katsina Ta Ayyana Gwamna Radda A Matsayin Dan Takara Daya Tilo A 2027

June 1, 2025
An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

An Karrama Dalibar Kaduna Da Ta Zo Ta Biyu A Gasar Karatun Alkur’ani Ta Duniya

June 1, 2025
Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

June 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.