• English
  • Business News
Sunday, June 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Ƙananan Hukumomin Zamfara

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Ƙananan Hukumomin Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka a Ƙananan Hukumomin Gummi, Bukkuyum da Maru.

Gwamnatin jihar ta zayyana jerin ayyuka da aka fi sani da ‘Ayyukan Ceto Zamfara’ don tunawa da shekara ɗaya na gwamnatin Dauda Lawal a kan mulki.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta jaddada cewa an fara ƙaddamar da ayyukan ne da makarantar Tsangaya ta zamani da ke Ƙaramar Hukumar Gummi.

gwamna

A cewarsa, an sanya wa makarantar Tsangayar sunan Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III OFR, wanda ya kasance babban baƙo na musamman a wajen buɗe makarantar.

Labarai Masu Nasaba

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

Sanarwar ta ƙara da cewa: “A yau ne gwamna Dauda Lawal ya fara rangaɗi a faɗin ƙananan hukumomin Zamfara 14 domin ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka da gwamnatinsa ta ƙaddamar a shekarar da ta gabata.

“Ayyukan an sanya su a matsayin ayyukan ceto, waɗanda suka mai da hankali kan wuraren da ke ƙara darajar rayuwar al’umma, ciki har da tsaro, kiwon lafiya, ilimi, da kayayyakin more rayuwa da sauransu.”

gwamna

Da yake gabatar da jawabinsa a ƙaramar hukumar Gummi, Gwamna Lawal ya jaddada cewa makarantar Tsangaya aiki ne da gwamnatinsa ta tsara kuma ta aiwatar a wani shiri na tabbatar da ilimin bai ɗaya ga dukkan yaran da suka isa zuwa makaranta a faɗin jihar.

“Tsarin ilimin Tsangaya ingantaccen tsarin ilimi ne a wannan yanki. Tsari ne da ake isar da tarbiyyar addini da kyawawan ɗabi’u ga duk wanda da ke cikinsa.

“Idan aka yi la’akari da muhimmancin tsarin ilimin Tsangaya ga al’ummarmu, za a ga cewa tsarin ya ƙunshi ilimin addinin Musulunci, wanda shi ne abin da Tsangaya ya mayar da hankali a kai, wanda kuma zai tafi daidai da ilimin zamani. Wannan yana nufin baiwa yaranmu ilimi da ƙwarewa don taimaka musu sanin yadda tsarin duniya ke tafiya a zamanance. Haɗa duka tsarin biyu, ita ce hanya mafi inganci ta kawo ƙarin ci gaba ga jama’armu da al’ummominmu.

gwamna

“Saboda haka tsarin zai haɗe karatun Islamiyya da ilimin zamani. Gwamnati kuma ta shigar da shi cikin Shirin Ilimi Na Kowa a jihar.

“Za a koyar da darussa kamar Ingilishi, Lissafi, Ilimin zamantakewa, da koyar da sana’o’i tare da ilimin addinin Islama, tare da haɓaka ƙwarewar yara da jin daɗin rayuwa.

“Wannan aikin ya ƙunshi gina ɗakunan kwanan ɗalibai guda tara, gidajen kwanan malamai, katangar za ta kewaye makaratar, wutar lantarki mai amfani da hasken rana, rijiyoyin burtsatse, kujeru da tebura, wuraren koyarwa da koyo da dai sauransu.

gwamna

“Bugu da ƙari, makarantar tana da cibiyar koyar da sana’o’i inda za a ba da horo a kan aikin kafinta, aikin katako, ɗinki, koyon aiki da kwamfuta da dai sauran su. Hakan zai ba su damar yin amfani da dabarun da suka samu tare da taimaka musu wajen samun abin dogaro da kai.”

A Nasarawa Burkullu, ƙaramar hukumar Bukkuyum, Gwamna Lawal ya ƙaddamar da babban asibitin da aka inganta daga cibiyar kula da lafiya ta matakin farko.

“Sabuwar ginin da aka inganta za ta samar da cikakkiyar aiki na kiwon lafiya kamar kulawar gaggawa, tiyata, kula da lafiyar mata da yara.

“Ayyukan da aka aiwatar sun haɗa da gina ƙarin gine-gine da kuma gyara waɗanda ake da su, kamar sashen keɓe masu lalura ta daman, wurin ajiyar gawa, sashen kula haɗari, ɗakin tiyata, ɗakunan tiyatar maza da mata, GOPD, ɗakin gwaje-gwaje, sashen magani, kula da mata masu juna biyu, da sashen kula da yara. Sauran sun haɗa da ɓangaren masu kula da asibiti, wuraren ma’aikata, masallatai, da rijiyoyin burtsatse.

A Ƙaramar Hukumar Maru, Gwamna Lawal ya tantance aikin gyaran babban asibitin Maru, wanda ya haɗa da gyaran dukkan gine-gine da samar da kayan aiki na zamani don bunƙasa ƙarfinta na samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AyyukaCi GabaGwamna Dauda LawalJihar ZamfaraShekara DayaTsaroZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zanga-Zanga Bayan Cire Sarki Aminu Ado, Abin Da Ya Kamata Ku Sani

Next Post

Ba Mu Jibge Dakarunmu Don Mayar Da Sarki Aminu Sarauta Ba – Sojoji

Related

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako
Labarai

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

8 hours ago
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80
Labarai

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

10 hours ago
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5
Manyan Labarai

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

15 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 

16 hours ago
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

16 hours ago
Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa
Labarai

Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa

18 hours ago
Next Post
Rundunar Sojoji Ta Karrama Jami’anta 10 Bisa Ƙwarewa A Yaƙi Da Ta’addanci

Ba Mu Jibge Dakarunmu Don Mayar Da Sarki Aminu Sarauta Ba - Sojoji

LABARAI MASU NASABA

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

June 21, 2025
CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

June 21, 2025
Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

June 21, 2025
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

June 21, 2025
Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

June 21, 2025
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

June 21, 2025
Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

June 21, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

June 21, 2025
Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

June 21, 2025
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

June 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.