ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Ƙananan Hukumomin Zamfara

by Leadership Hausa
2 years ago
gwamna

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka a Ƙananan Hukumomin Gummi, Bukkuyum da Maru.

Gwamnatin jihar ta zayyana jerin ayyuka da aka fi sani da ‘Ayyukan Ceto Zamfara’ don tunawa da shekara ɗaya na gwamnatin Dauda Lawal a kan mulki.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta jaddada cewa an fara ƙaddamar da ayyukan ne da makarantar Tsangaya ta zamani da ke Ƙaramar Hukumar Gummi.

ADVERTISEMENT

gwamna

A cewarsa, an sanya wa makarantar Tsangayar sunan Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III OFR, wanda ya kasance babban baƙo na musamman a wajen buɗe makarantar.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Sanarwar ta ƙara da cewa: “A yau ne gwamna Dauda Lawal ya fara rangaɗi a faɗin ƙananan hukumomin Zamfara 14 domin ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka da gwamnatinsa ta ƙaddamar a shekarar da ta gabata.

“Ayyukan an sanya su a matsayin ayyukan ceto, waɗanda suka mai da hankali kan wuraren da ke ƙara darajar rayuwar al’umma, ciki har da tsaro, kiwon lafiya, ilimi, da kayayyakin more rayuwa da sauransu.”

gwamna

Da yake gabatar da jawabinsa a ƙaramar hukumar Gummi, Gwamna Lawal ya jaddada cewa makarantar Tsangaya aiki ne da gwamnatinsa ta tsara kuma ta aiwatar a wani shiri na tabbatar da ilimin bai ɗaya ga dukkan yaran da suka isa zuwa makaranta a faɗin jihar.

“Tsarin ilimin Tsangaya ingantaccen tsarin ilimi ne a wannan yanki. Tsari ne da ake isar da tarbiyyar addini da kyawawan ɗabi’u ga duk wanda da ke cikinsa.

“Idan aka yi la’akari da muhimmancin tsarin ilimin Tsangaya ga al’ummarmu, za a ga cewa tsarin ya ƙunshi ilimin addinin Musulunci, wanda shi ne abin da Tsangaya ya mayar da hankali a kai, wanda kuma zai tafi daidai da ilimin zamani. Wannan yana nufin baiwa yaranmu ilimi da ƙwarewa don taimaka musu sanin yadda tsarin duniya ke tafiya a zamanance. Haɗa duka tsarin biyu, ita ce hanya mafi inganci ta kawo ƙarin ci gaba ga jama’armu da al’ummominmu.

gwamna

“Saboda haka tsarin zai haɗe karatun Islamiyya da ilimin zamani. Gwamnati kuma ta shigar da shi cikin Shirin Ilimi Na Kowa a jihar.

“Za a koyar da darussa kamar Ingilishi, Lissafi, Ilimin zamantakewa, da koyar da sana’o’i tare da ilimin addinin Islama, tare da haɓaka ƙwarewar yara da jin daɗin rayuwa.

“Wannan aikin ya ƙunshi gina ɗakunan kwanan ɗalibai guda tara, gidajen kwanan malamai, katangar za ta kewaye makaratar, wutar lantarki mai amfani da hasken rana, rijiyoyin burtsatse, kujeru da tebura, wuraren koyarwa da koyo da dai sauransu.

gwamna

“Bugu da ƙari, makarantar tana da cibiyar koyar da sana’o’i inda za a ba da horo a kan aikin kafinta, aikin katako, ɗinki, koyon aiki da kwamfuta da dai sauran su. Hakan zai ba su damar yin amfani da dabarun da suka samu tare da taimaka musu wajen samun abin dogaro da kai.”

A Nasarawa Burkullu, ƙaramar hukumar Bukkuyum, Gwamna Lawal ya ƙaddamar da babban asibitin da aka inganta daga cibiyar kula da lafiya ta matakin farko.

“Sabuwar ginin da aka inganta za ta samar da cikakkiyar aiki na kiwon lafiya kamar kulawar gaggawa, tiyata, kula da lafiyar mata da yara.

“Ayyukan da aka aiwatar sun haɗa da gina ƙarin gine-gine da kuma gyara waɗanda ake da su, kamar sashen keɓe masu lalura ta daman, wurin ajiyar gawa, sashen kula haɗari, ɗakin tiyata, ɗakunan tiyatar maza da mata, GOPD, ɗakin gwaje-gwaje, sashen magani, kula da mata masu juna biyu, da sashen kula da yara. Sauran sun haɗa da ɓangaren masu kula da asibiti, wuraren ma’aikata, masallatai, da rijiyoyin burtsatse.

A Ƙaramar Hukumar Maru, Gwamna Lawal ya tantance aikin gyaran babban asibitin Maru, wanda ya haɗa da gyaran dukkan gine-gine da samar da kayan aiki na zamani don bunƙasa ƙarfinta na samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga al’umma.

gwamna
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura

MASU ALAKA

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Labarai

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu
Manyan Labarai

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Next Post
Rundunar Sojoji Ta Karrama Jami’anta 10 Bisa Ƙwarewa A Yaƙi Da Ta’addanci

Ba Mu Jibge Dakarunmu Don Mayar Da Sarki Aminu Sarauta Ba - Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026
Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

Taron Kolin Urumqi Ya Mayar Da Hankali Kan Kwarewar Shugabanci A Xinjiang Da Muhimmancinta Ga Duniya

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.