ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya A Mulki: Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Ƙananan Hukumomin Zamfara

by Leadership Hausa
2 years ago
gwamna

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka a Ƙananan Hukumomin Gummi, Bukkuyum da Maru.

Gwamnatin jihar ta zayyana jerin ayyuka da aka fi sani da ‘Ayyukan Ceto Zamfara’ don tunawa da shekara ɗaya na gwamnatin Dauda Lawal a kan mulki.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta jaddada cewa an fara ƙaddamar da ayyukan ne da makarantar Tsangaya ta zamani da ke Ƙaramar Hukumar Gummi.

ADVERTISEMENT

gwamna

A cewarsa, an sanya wa makarantar Tsangayar sunan Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III OFR, wanda ya kasance babban baƙo na musamman a wajen buɗe makarantar.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Sanarwar ta ƙara da cewa: “A yau ne gwamna Dauda Lawal ya fara rangaɗi a faɗin ƙananan hukumomin Zamfara 14 domin ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka da gwamnatinsa ta ƙaddamar a shekarar da ta gabata.

“Ayyukan an sanya su a matsayin ayyukan ceto, waɗanda suka mai da hankali kan wuraren da ke ƙara darajar rayuwar al’umma, ciki har da tsaro, kiwon lafiya, ilimi, da kayayyakin more rayuwa da sauransu.”

gwamna

Da yake gabatar da jawabinsa a ƙaramar hukumar Gummi, Gwamna Lawal ya jaddada cewa makarantar Tsangaya aiki ne da gwamnatinsa ta tsara kuma ta aiwatar a wani shiri na tabbatar da ilimin bai ɗaya ga dukkan yaran da suka isa zuwa makaranta a faɗin jihar.

“Tsarin ilimin Tsangaya ingantaccen tsarin ilimi ne a wannan yanki. Tsari ne da ake isar da tarbiyyar addini da kyawawan ɗabi’u ga duk wanda da ke cikinsa.

“Idan aka yi la’akari da muhimmancin tsarin ilimin Tsangaya ga al’ummarmu, za a ga cewa tsarin ya ƙunshi ilimin addinin Musulunci, wanda shi ne abin da Tsangaya ya mayar da hankali a kai, wanda kuma zai tafi daidai da ilimin zamani. Wannan yana nufin baiwa yaranmu ilimi da ƙwarewa don taimaka musu sanin yadda tsarin duniya ke tafiya a zamanance. Haɗa duka tsarin biyu, ita ce hanya mafi inganci ta kawo ƙarin ci gaba ga jama’armu da al’ummominmu.

gwamna

“Saboda haka tsarin zai haɗe karatun Islamiyya da ilimin zamani. Gwamnati kuma ta shigar da shi cikin Shirin Ilimi Na Kowa a jihar.

“Za a koyar da darussa kamar Ingilishi, Lissafi, Ilimin zamantakewa, da koyar da sana’o’i tare da ilimin addinin Islama, tare da haɓaka ƙwarewar yara da jin daɗin rayuwa.

“Wannan aikin ya ƙunshi gina ɗakunan kwanan ɗalibai guda tara, gidajen kwanan malamai, katangar za ta kewaye makaratar, wutar lantarki mai amfani da hasken rana, rijiyoyin burtsatse, kujeru da tebura, wuraren koyarwa da koyo da dai sauransu.

gwamna

“Bugu da ƙari, makarantar tana da cibiyar koyar da sana’o’i inda za a ba da horo a kan aikin kafinta, aikin katako, ɗinki, koyon aiki da kwamfuta da dai sauran su. Hakan zai ba su damar yin amfani da dabarun da suka samu tare da taimaka musu wajen samun abin dogaro da kai.”

A Nasarawa Burkullu, ƙaramar hukumar Bukkuyum, Gwamna Lawal ya ƙaddamar da babban asibitin da aka inganta daga cibiyar kula da lafiya ta matakin farko.

“Sabuwar ginin da aka inganta za ta samar da cikakkiyar aiki na kiwon lafiya kamar kulawar gaggawa, tiyata, kula da lafiyar mata da yara.

“Ayyukan da aka aiwatar sun haɗa da gina ƙarin gine-gine da kuma gyara waɗanda ake da su, kamar sashen keɓe masu lalura ta daman, wurin ajiyar gawa, sashen kula haɗari, ɗakin tiyata, ɗakunan tiyatar maza da mata, GOPD, ɗakin gwaje-gwaje, sashen magani, kula da mata masu juna biyu, da sashen kula da yara. Sauran sun haɗa da ɓangaren masu kula da asibiti, wuraren ma’aikata, masallatai, da rijiyoyin burtsatse.

A Ƙaramar Hukumar Maru, Gwamna Lawal ya tantance aikin gyaran babban asibitin Maru, wanda ya haɗa da gyaran dukkan gine-gine da samar da kayan aiki na zamani don bunƙasa ƙarfinta na samar da ingantattun ayyukan kiwon lafiya ga al’umma.

gwamna
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Rundunar Sojoji Ta Karrama Jami’anta 10 Bisa Ƙwarewa A Yaƙi Da Ta’addanci

Ba Mu Jibge Dakarunmu Don Mayar Da Sarki Aminu Sarauta Ba - Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.