• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya A Ofis: An Buɗe Gasar Cin Kofin Babban Hafsan Sojojin Nijeriya A Katsina

byMuhammad and El-Zaharadeen Umar
1 year ago
Katsina

An buɗe gasar kwallon kafa ta cin kofin baban Hafsan Sojojin Nijeriya a Katsina domin taya shi murnar cika shekara ɗaya a ofis.

An shirya gasar ne da nufin ƙara kyautata alaƙa a tsakanin matasa, inda kulob 32 za su fafata a filin wasa na birget na 17 da kuma filin wasa na KCK da ke Katsina.

  • Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki, Sun Yi Kisa, Sun Kwashe Mutune 22 A Katsina
  • Jami’ar ‘Yar’aduwa Ta Katsina Ta Kama Hanyar Rugujewa – ASUU

Tunda farko da yake jawabi a taron bikin buɗe gasar, baban kwamanda mai kula da Birget na 17 da ke Katsina, Ibikunle Ademola Ajose, ya bayyana cewa shirya irin waɗannan wassani abu ne mai kyau, domin ta haka ne za a ƙara kulla alaƙa a tsakanin matasa.

Ya ƙara da cewa waɗanda suka shirya wannan gasa sun yi hangen nesa, kuma sun yi abin da yakamata a lokacin da ya dace, musamman don tunawa da shi babban Hafsan Sojojin Nijeriya, Christopher Gwabin Musa
.
A cewar baban kwamanda mai kula da birget na 17, Ibikunle Ademola, yana fatan za a yi wannan gasa a kammala cikin nasara ba tare da wata matsala ba, musamman tun da abin ya haɗa da matasa.

A wajen wannan biki dai kungiyoyin kwallo guda biyu ne suka kara, wato Sarkin Yaki da kuma K-Soro, wanda bayan an fafata daga ƙarshe kungiyar kwallon kafa ta K-Soro ta samu nasara da bugun daga kai sai mia tsaron gida.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Yanzu dai za a ci gaba da waɗannan wassani a filin wasa na KCK, inda ake sa ran sauran kolab ɗin za su nuna bajintar su domin samun nasara a ƙarshen gasar.

A nasa jawabin, shugaban shirya wannan gasa domin taya baban Hafsan Sojojin Nijeriya, Janar Christopher Gwabin Musa, Malam Lawal BK ya bayyana cewa sun yi tunanin shirya gasar ne domin sada zumunci a tsakanin matasa.

Ya ƙara da cewa yanzu hanya mafi sauki da za a ja matasa a jiki, ita ce shirya irin wannan gasa, ya ce babu komai za a ɗora matasa a wata turba wadda za ta hana su yin tunanin abubuwa marasa kyau.

“Matasan mu yanzu idan ka kyale su, ba zamu yi tunanin irin wanda yakamata ba, amma shi wasan ƙwallon ƙafa abu ne da matasa ke so, to ko ba komi ka ɗebe masu kewa sannan ka sanya su nishadi ” inji shi

Kamar yadda aka tsara kungiyoyin kwallo kafa guda 32 ne za su fafata kuma wasa daya ne za a riƙa bugawa duk wanda ya samu nasara zai hau mataki na gaba.

Kazalika an ware kyaututtuka masu yawa wanda a ƙarshen gasar za a rabawa kungiyar da ta samu nasara.

Sauran kungiyoyin kwallon kafar da za su taka leda sun haɗa da Katsina Boys da Shooting Star da Durbi Strikers da KKT Strikers da Home Boys da Gawo Prof. da kuma Kamuwa United da Manaco ATC da dai sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Sojoji Da Mafarauta Sun Dakile Shirin ‘Yan Ta’adda Na Lalata Falwayar Wutar Lantarki A Yobe

Sojoji Da Mafarauta Sun Dakile Shirin ‘Yan Ta'adda Na Lalata Falwayar Wutar Lantarki A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version