ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Ɗaya A Ofis: An Buɗe Gasar Cin Kofin Babban Hafsan Sojojin Nijeriya A Katsina

by Muhammad and El-Zaharadeen Umar
2 years ago
Katsina

An buɗe gasar kwallon kafa ta cin kofin baban Hafsan Sojojin Nijeriya a Katsina domin taya shi murnar cika shekara ɗaya a ofis.

An shirya gasar ne da nufin ƙara kyautata alaƙa a tsakanin matasa, inda kulob 32 za su fafata a filin wasa na birget na 17 da kuma filin wasa na KCK da ke Katsina.

  • Ƴan Bindiga Sun Kai Farmaki, Sun Yi Kisa, Sun Kwashe Mutune 22 A Katsina
  • Jami’ar ‘Yar’aduwa Ta Katsina Ta Kama Hanyar Rugujewa – ASUU

Tunda farko da yake jawabi a taron bikin buɗe gasar, baban kwamanda mai kula da Birget na 17 da ke Katsina, Ibikunle Ademola Ajose, ya bayyana cewa shirya irin waɗannan wassani abu ne mai kyau, domin ta haka ne za a ƙara kulla alaƙa a tsakanin matasa.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa waɗanda suka shirya wannan gasa sun yi hangen nesa, kuma sun yi abin da yakamata a lokacin da ya dace, musamman don tunawa da shi babban Hafsan Sojojin Nijeriya, Christopher Gwabin Musa
.
A cewar baban kwamanda mai kula da birget na 17, Ibikunle Ademola, yana fatan za a yi wannan gasa a kammala cikin nasara ba tare da wata matsala ba, musamman tun da abin ya haɗa da matasa.

A wajen wannan biki dai kungiyoyin kwallo guda biyu ne suka kara, wato Sarkin Yaki da kuma K-Soro, wanda bayan an fafata daga ƙarshe kungiyar kwallon kafa ta K-Soro ta samu nasara da bugun daga kai sai mia tsaron gida.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Yanzu dai za a ci gaba da waɗannan wassani a filin wasa na KCK, inda ake sa ran sauran kolab ɗin za su nuna bajintar su domin samun nasara a ƙarshen gasar.

A nasa jawabin, shugaban shirya wannan gasa domin taya baban Hafsan Sojojin Nijeriya, Janar Christopher Gwabin Musa, Malam Lawal BK ya bayyana cewa sun yi tunanin shirya gasar ne domin sada zumunci a tsakanin matasa.

Ya ƙara da cewa yanzu hanya mafi sauki da za a ja matasa a jiki, ita ce shirya irin wannan gasa, ya ce babu komai za a ɗora matasa a wata turba wadda za ta hana su yin tunanin abubuwa marasa kyau.

“Matasan mu yanzu idan ka kyale su, ba zamu yi tunanin irin wanda yakamata ba, amma shi wasan ƙwallon ƙafa abu ne da matasa ke so, to ko ba komi ka ɗebe masu kewa sannan ka sanya su nishadi ” inji shi

Kamar yadda aka tsara kungiyoyin kwallo kafa guda 32 ne za su fafata kuma wasa daya ne za a riƙa bugawa duk wanda ya samu nasara zai hau mataki na gaba.

Kazalika an ware kyaututtuka masu yawa wanda a ƙarshen gasar za a rabawa kungiyar da ta samu nasara.

Sauran kungiyoyin kwallon kafar da za su taka leda sun haɗa da Katsina Boys da Shooting Star da Durbi Strikers da KKT Strikers da Home Boys da Gawo Prof. da kuma Kamuwa United da Manaco ATC da dai sauransu.

Katsina
Muhammad
+ posts Bio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa
Katsina
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Sojoji Da Mafarauta Sun Dakile Shirin ‘Yan Ta’adda Na Lalata Falwayar Wutar Lantarki A Yobe

Sojoji Da Mafarauta Sun Dakile Shirin ‘Yan Ta'adda Na Lalata Falwayar Wutar Lantarki A Yobe

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.