ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar ‘Yar’aduwa Ta Katsina Ta Kama Hanyar Rugujewa – ASUU

…Ku Rika Bincike Kafin Ku Yi Magana, Gwamnatin Katsina Ta Mayar Da Martani

by Sulaiman and El-Zaharadeen Umar
2 years ago
ASUU

Jami’ar Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina ta kama hanyar rugujewa sakamakon rashin isasun kudaden gudanarwa daga gwamnatin jihar Katsina.

Shugaban kungiyar Malaman jami’a ta ASUU reshen UMYUK Dakta Murtala Abdu Kwara ya bayyana haka a wani taron manema labarai a Katsina.

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Jajanta Wa Mataimakin Gwamnan Neja Kan Rasuwar Matarsa
  • Kanana Hukumomin Kano Da Jigawa 23 Na Kan Gaba Wajen Fuskantar Ambaliyar Ruwa – NEMA

Ya kara da cewa maganar da ake yanzu jami’ar na kokowa da matsalar rashin wadatattun kudaden tafiyar da bangaren ma’aikata da kuma dalibai.

ADVERTISEMENT

A cewar Dakta Murtala Abdu Kwara gwamna Malam Dikko Umar Radda na bai wa jami’ar Naira miliyan 7 duk wata a matsayin kudin gudanarwa a maimakon miliyan 16 da ake bata a gwamantin da ta gabata.
“Wannan jami’a ta fara karatu da tsangaya uku ne kacal kuma kudin gudanarwarta miliyan 16 yanzu kuma muna da tsangaya 9 amma kudin gudanarwa ba su canza ba, suna nan miliyan 7” in ji shi

Ya ce halin da jami’ar take ciki a halin yanzu ta sa dole aka dakatar da bai wa wasu sassanta kudaden gudanarwa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Haka kuma ya koka a kan yadda Gwaman Dikko Umar Radda ya ki aiwatar da kaso 25/35 na albashin ma’aikata wanda ya ce wasu jami’o’i tuni sun fara aiwatarwa/

Kazalika Dakta Murtala Abdu Kwara ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Katsina ta sake duba tsarin biyan kudaden gudanarwa na jami’ar domin ceto ta daga rugujewa.

…Ku Rika Bincike Kafin Ku Yi Magana, Gwamnatin Katsina Ta Mayar Da Martani

Gwamnatin jihar Katsina ta maida wa Kungiyar Malaman jami’a ta ASUU reshen Jami’ar Yar’adua da ke Katsina martani dangane da ikirarin da ta yi na cewa jami’ar ta kama hanyar durkushewa.

Kwamishinan ma’aikatan ilimi mai zurfi da kula da kere-kere Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya maida martanin da cewa ba gwamnatinsu ba ce ta rage kudaden gudanarwar jami’ar ba.

“Wannan gwamnatin karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda ba ta taba rage ko naira ba daga kudaden gudanarwa da ake ba Jami’ar Yar’adua kuma ba a taba fashin biyan su ba.”in ji shi.

Kwamishinan wanda ya ce shi daya ne daga cikin Malaman jami’ar kafin ya samu mukami ya san duk abin da ke faruwa yana da masaniyar musamman tafiyar da sha’anin jami’ar.

Kazalika ya yi kira ga kungiyar ASUU da ta koma jami’ar ta bincika ta gani daga yaushe ne aka rage wadancan kudaden da suke magana, ba wai su fito a kafafen yada labarai ba suna fadin abin da ba haka yake ba.

Sannan ya kara da cewa babu wanda ya taba rubuta wa gwamnati cewa kudaden gudanarwa da ake ba jami’ar da sauran manyan makarantu ba sa isarsu, babu wanda ya taba sanar da gwamnati.

“Kuma ina son jama’a da su gane, ASUU sun ce adadin dalibai da tsangaya sun karu, to su bayyana wa duniya adadin kudaden shiga da suke samu a yanzu kowa ya sani.

A cewarsa, ko naira daya ba sa ba gwamnatin jihar Katsina, su ke tara kudinsu, su ke kashe su, saboda haka ya ce su je su bincika tun shekarar 2015 aka fara zabtare kudaden gudanarwa na jami’ar da sauran makarantu guda biyar.

Da kwamishinan ya juya kan korafin da kungiyar ASUU ta yi na cewa gwamnatin tarayya ta fara aiwatar da shirin karin albashi na kaso 25/35, ya ce yanzu haka maganar tana kan teburin Gwamna Dikko Umar Radda jira ake ya ba da umarni.

Ya kara da cewa maganar karin albashi da kungiyar kwadago ta bijiro da ita, ta tsayar da batun, amma tuni an gama wannan maganar, yana mai cewa ya sanar da duk manyan makarantun da suke karkashin kulawar ma’aikatarsa, inda aka kwana da inda aka tashi a kan batun karin albashi, amma ba wai an fasa ba ne.

Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya ce akwai abubuwa da yawa da gwamnatin jihar Katsina ta shirya yi bangaren ilimi wanda ya ce wasu ba zai fade su ba yanzu, sai nan gaba saboda mahimmancinsu ga jihar Katsina.

Ya kuma kalubalanci jami’ar Yar’adua wanda ya ce Gwamna Dikko Umar Radda ya yi alkawarin cewa duk dalibin da ya fita da digiri mai daraja ta farko zai dauke shi aiki ba tare da bata lokaci ba, amma ya ce kusan wata biyu da yin wannan batu har gobe jami’ar ba ta aiko a rubuce ba tana son a aiwatar da wancan alkawari.

Ya kara da cewa sai dai su daliban ne suka tunkari ma’aikatar ilimi mai zurfi da kula da kere-kere domin jin inda aka kwana, amma daga jami’ar babu wanda ya rubutu a hukumance.

ASUU
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
ASUU
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Wang Yi: Ziyarar Xi Ya Zurfafa Dangantakar Kasashe Makwabta

Wang Yi: Ziyarar Xi Ya Zurfafa Dangantakar Kasashe Makwabta

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.