ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar ‘Yar’aduwa Ta Katsina Ta Kama Hanyar Rugujewa – ASUU

…Ku Rika Bincike Kafin Ku Yi Magana, Gwamnatin Katsina Ta Mayar Da Martani

by Sulaiman and El-Zaharadeen Umar
2 years ago
ASUU

Jami’ar Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina ta kama hanyar rugujewa sakamakon rashin isasun kudaden gudanarwa daga gwamnatin jihar Katsina.

Shugaban kungiyar Malaman jami’a ta ASUU reshen UMYUK Dakta Murtala Abdu Kwara ya bayyana haka a wani taron manema labarai a Katsina.

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Jajanta Wa Mataimakin Gwamnan Neja Kan Rasuwar Matarsa
  • Kanana Hukumomin Kano Da Jigawa 23 Na Kan Gaba Wajen Fuskantar Ambaliyar Ruwa – NEMA

Ya kara da cewa maganar da ake yanzu jami’ar na kokowa da matsalar rashin wadatattun kudaden tafiyar da bangaren ma’aikata da kuma dalibai.

ADVERTISEMENT

A cewar Dakta Murtala Abdu Kwara gwamna Malam Dikko Umar Radda na bai wa jami’ar Naira miliyan 7 duk wata a matsayin kudin gudanarwa a maimakon miliyan 16 da ake bata a gwamantin da ta gabata.
“Wannan jami’a ta fara karatu da tsangaya uku ne kacal kuma kudin gudanarwarta miliyan 16 yanzu kuma muna da tsangaya 9 amma kudin gudanarwa ba su canza ba, suna nan miliyan 7” in ji shi

Ya ce halin da jami’ar take ciki a halin yanzu ta sa dole aka dakatar da bai wa wasu sassanta kudaden gudanarwa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Haka kuma ya koka a kan yadda Gwaman Dikko Umar Radda ya ki aiwatar da kaso 25/35 na albashin ma’aikata wanda ya ce wasu jami’o’i tuni sun fara aiwatarwa/

Kazalika Dakta Murtala Abdu Kwara ya yi kira ga Gwamnatin Jihar Katsina ta sake duba tsarin biyan kudaden gudanarwa na jami’ar domin ceto ta daga rugujewa.

…Ku Rika Bincike Kafin Ku Yi Magana, Gwamnatin Katsina Ta Mayar Da Martani

Gwamnatin jihar Katsina ta maida wa Kungiyar Malaman jami’a ta ASUU reshen Jami’ar Yar’adua da ke Katsina martani dangane da ikirarin da ta yi na cewa jami’ar ta kama hanyar durkushewa.

Kwamishinan ma’aikatan ilimi mai zurfi da kula da kere-kere Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya maida martanin da cewa ba gwamnatinsu ba ce ta rage kudaden gudanarwar jami’ar ba.

“Wannan gwamnatin karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda ba ta taba rage ko naira ba daga kudaden gudanarwa da ake ba Jami’ar Yar’adua kuma ba a taba fashin biyan su ba.”in ji shi.

Kwamishinan wanda ya ce shi daya ne daga cikin Malaman jami’ar kafin ya samu mukami ya san duk abin da ke faruwa yana da masaniyar musamman tafiyar da sha’anin jami’ar.

Kazalika ya yi kira ga kungiyar ASUU da ta koma jami’ar ta bincika ta gani daga yaushe ne aka rage wadancan kudaden da suke magana, ba wai su fito a kafafen yada labarai ba suna fadin abin da ba haka yake ba.

Sannan ya kara da cewa babu wanda ya taba rubuta wa gwamnati cewa kudaden gudanarwa da ake ba jami’ar da sauran manyan makarantu ba sa isarsu, babu wanda ya taba sanar da gwamnati.

“Kuma ina son jama’a da su gane, ASUU sun ce adadin dalibai da tsangaya sun karu, to su bayyana wa duniya adadin kudaden shiga da suke samu a yanzu kowa ya sani.

A cewarsa, ko naira daya ba sa ba gwamnatin jihar Katsina, su ke tara kudinsu, su ke kashe su, saboda haka ya ce su je su bincika tun shekarar 2015 aka fara zabtare kudaden gudanarwa na jami’ar da sauran makarantu guda biyar.

Da kwamishinan ya juya kan korafin da kungiyar ASUU ta yi na cewa gwamnatin tarayya ta fara aiwatar da shirin karin albashi na kaso 25/35, ya ce yanzu haka maganar tana kan teburin Gwamna Dikko Umar Radda jira ake ya ba da umarni.

Ya kara da cewa maganar karin albashi da kungiyar kwadago ta bijiro da ita, ta tsayar da batun, amma tuni an gama wannan maganar, yana mai cewa ya sanar da duk manyan makarantun da suke karkashin kulawar ma’aikatarsa, inda aka kwana da inda aka tashi a kan batun karin albashi, amma ba wai an fasa ba ne.

Ferfasa Abdulhamid Ahmad ya ce akwai abubuwa da yawa da gwamnatin jihar Katsina ta shirya yi bangaren ilimi wanda ya ce wasu ba zai fade su ba yanzu, sai nan gaba saboda mahimmancinsu ga jihar Katsina.

Ya kuma kalubalanci jami’ar Yar’adua wanda ya ce Gwamna Dikko Umar Radda ya yi alkawarin cewa duk dalibin da ya fita da digiri mai daraja ta farko zai dauke shi aiki ba tare da bata lokaci ba, amma ya ce kusan wata biyu da yin wannan batu har gobe jami’ar ba ta aiko a rubuce ba tana son a aiwatar da wancan alkawari.

Ya kara da cewa sai dai su daliban ne suka tunkari ma’aikatar ilimi mai zurfi da kula da kere-kere domin jin inda aka kwana, amma daga jami’ar babu wanda ya rubutu a hukumance.

ASUU
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
ASUU
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Wang Yi: Ziyarar Xi Ya Zurfafa Dangantakar Kasashe Makwabta

Wang Yi: Ziyarar Xi Ya Zurfafa Dangantakar Kasashe Makwabta

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.