• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara 10 Da Sace ‘Yan Matan Chibok: Gidauniya Ta Bayyana Abubuwan Alhini

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Labarai
0
Shekara 10 Da Sace ‘Yan Matan Chibok: Gidauniya Ta Bayyana Abubuwan Alhini
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekara 10 kenan da sace ‘yan mata 276 na makarantar sakandaren gwamnati da ke garin Chibok a Jihar Borno, an fitar da wani sabon rahoto da ke nuna cewa ‘yan mata 21 daga cikin wadanda aka sako ya zuwa yanzu sun dawo gida tare da yara 34.

Wannan yana cikin rahoton da Gidauniyar Murtala Muhammed (MMF) ta fitar ta kuma ta raba wa manema labarai a karshen mako a Abuja.

  • Bangaren Amurka Ya Mayar Wa Bangaren Sin Da Kayayyakin Tarihi 38 Da Suka Bata Daga Sin
  • Shari’ar Zargin Karkatar Da Dukiyar Al’umma: Ganduje Da Iyalansa Ba Su Halarci Kotu Ba

Kamar yadda gidauniyar ta ce, rahoton an yi shi ne domin tunawa da cika shakara 10 da sace ‘yan matan. Rahoton ya kuma tabbatar da cin zarafi da auren dole da ‘yan matan suka fuskanta a lokacin da suke tsare a hannun ‘yan ta’addan.

Haka kuma rahoton na gidauniyar ya kara bayyana cewa iyayen daliban aka sace su 48 ne suka mutu. Sauran iyayen daliban da ke raye kuma na rayuwa cikin tashin hankali da fargabar rashin sanin halin da ‘ya’yansu ke ciki.

Babban Daraktan gidauniyar MMF, Dakta Aisha Muhammad-Oyebode wacce ta gabatar da rahoton ta bayyana cewa, gidauniyar ta lissafa wasu muhimman shawarwari guda 10.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Gidauniyar ta ce ya kamata gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da kasashen duniya su ba da fifiko a kan wadannan shawarwari. Shawarwarin sun hada da, daukar ingantattun matakan tsaro, shirye-shiryen tallafa wa kuyuka da tsarin ankararwa cikin gaggawa dangane da barazanar tsaro.

Ta ce, “A cikin shekara 10 tun lokacin da aka yi garkuwa da ‘yan matan Chibok ya janyo fusata al’ummar duniya gaba daya, kowani al’amari ya sauya a Nijeriya, inda masu garkuwa da mutane ke ci gaba da cin karansu babu babbaka na tsawon shekaru masu yawa.

“A daidai lokacin da Nijeriya ke fama da annoban garkuwa da mutane wanda ba ta nuna alaman raguwa ba, muna kira ga hukumomin Nijeriya da na kasa da kasa su dauki muhimman matakai domin magance abubuwan da ke janyo rikice-rikice da tashin hankali kan mata, wadanda suka hada da fatara, rashin natsuwa da tabarbarewar tattalin arziki.

“Rahoton ya gano cewa cikin 91 na daliban makarantar guda 276 har yanzu ba su san inda aka dosa ba.

“Rahoton ya kuma bayyana cewa ‘yan matan Chibok 21 da aka sako sun samu sun dawo da yara 34, wanda ya nuna sun fuskanci cin zarafi na jin jima’I da su da kuma tilasta musu yin auren dole lokacin da suke tsare.

“Rahoton MMF ya bayar da shawarar cewa a yi kokarin magance tushen yin garkuwa da mutane, sannan ya bukaci karfafa hadin gwiwa na kasa da kasa wajen daukar matakan kawo karshen lamarin.”

Ta kuma bayar da shawarar a dauki matakin tabbatar da hukunta wadanda ke da hannu kan wannan mummunan labari komin matsayin da suke da shi doka ta yi aiki a kan kowa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wang Yi: Amurka Ba Ta Da Alfarma Ko Gatan Kin Biyayya Ga Dokokin Kasa Da Kasa

Next Post

Likitocin Kasar Sin Sun Taimakawa Al’ummun Saliyo Da Dabarun Yaki Da Malaria

Related

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

9 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

9 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

11 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

14 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

14 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

15 hours ago
Next Post
Likitocin Kasar Sin Sun Taimakawa Al’ummun Saliyo Da Dabarun Yaki Da Malaria

Likitocin Kasar Sin Sun Taimakawa Al’ummun Saliyo Da Dabarun Yaki Da Malaria

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.