ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara 10 Da Sace ‘Yan Matan Chibok: Gidauniya Ta Bayyana Abubuwan Alhini

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Chibok

Shekara 10 kenan da sace ‘yan mata 276 na makarantar sakandaren gwamnati da ke garin Chibok a Jihar Borno, an fitar da wani sabon rahoto da ke nuna cewa ‘yan mata 21 daga cikin wadanda aka sako ya zuwa yanzu sun dawo gida tare da yara 34.

Wannan yana cikin rahoton da Gidauniyar Murtala Muhammed (MMF) ta fitar ta kuma ta raba wa manema labarai a karshen mako a Abuja.

  • Bangaren Amurka Ya Mayar Wa Bangaren Sin Da Kayayyakin Tarihi 38 Da Suka Bata Daga Sin
  • Shari’ar Zargin Karkatar Da Dukiyar Al’umma: Ganduje Da Iyalansa Ba Su Halarci Kotu Ba

Kamar yadda gidauniyar ta ce, rahoton an yi shi ne domin tunawa da cika shakara 10 da sace ‘yan matan. Rahoton ya kuma tabbatar da cin zarafi da auren dole da ‘yan matan suka fuskanta a lokacin da suke tsare a hannun ‘yan ta’addan.

ADVERTISEMENT

Haka kuma rahoton na gidauniyar ya kara bayyana cewa iyayen daliban aka sace su 48 ne suka mutu. Sauran iyayen daliban da ke raye kuma na rayuwa cikin tashin hankali da fargabar rashin sanin halin da ‘ya’yansu ke ciki.

Babban Daraktan gidauniyar MMF, Dakta Aisha Muhammad-Oyebode wacce ta gabatar da rahoton ta bayyana cewa, gidauniyar ta lissafa wasu muhimman shawarwari guda 10.

LABARAI MASU NASABA

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Gidauniyar ta ce ya kamata gwamnatin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu da kasashen duniya su ba da fifiko a kan wadannan shawarwari. Shawarwarin sun hada da, daukar ingantattun matakan tsaro, shirye-shiryen tallafa wa kuyuka da tsarin ankararwa cikin gaggawa dangane da barazanar tsaro.

Ta ce, “A cikin shekara 10 tun lokacin da aka yi garkuwa da ‘yan matan Chibok ya janyo fusata al’ummar duniya gaba daya, kowani al’amari ya sauya a Nijeriya, inda masu garkuwa da mutane ke ci gaba da cin karansu babu babbaka na tsawon shekaru masu yawa.

“A daidai lokacin da Nijeriya ke fama da annoban garkuwa da mutane wanda ba ta nuna alaman raguwa ba, muna kira ga hukumomin Nijeriya da na kasa da kasa su dauki muhimman matakai domin magance abubuwan da ke janyo rikice-rikice da tashin hankali kan mata, wadanda suka hada da fatara, rashin natsuwa da tabarbarewar tattalin arziki.

“Rahoton ya gano cewa cikin 91 na daliban makarantar guda 276 har yanzu ba su san inda aka dosa ba.

“Rahoton ya kuma bayyana cewa ‘yan matan Chibok 21 da aka sako sun samu sun dawo da yara 34, wanda ya nuna sun fuskanci cin zarafi na jin jima’I da su da kuma tilasta musu yin auren dole lokacin da suke tsare.

“Rahoton MMF ya bayar da shawarar cewa a yi kokarin magance tushen yin garkuwa da mutane, sannan ya bukaci karfafa hadin gwiwa na kasa da kasa wajen daukar matakan kawo karshen lamarin.”

Ta kuma bayar da shawarar a dauki matakin tabbatar da hukunta wadanda ke da hannu kan wannan mummunan labari komin matsayin da suke da shi doka ta yi aiki a kan kowa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Next Post
Likitocin Kasar Sin Sun Taimakawa Al’ummun Saliyo Da Dabarun Yaki Da Malaria

Likitocin Kasar Sin Sun Taimakawa Al’ummun Saliyo Da Dabarun Yaki Da Malaria

LABARAI MASU NASABA

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.