ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Daya Ta Mulki: Zaki Da Dacin Gwamnatin Tinubu

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Tinubu

A lokacin da Shugaba kasa, Bola Tinubu ya dare kan karagar mulkin Nijeriya, ‘yan Nijeriya da dama suka fara fatan ganin wahalhalun da suke ciki za su kau, musamman ganin cewa a wancan lokacin gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ta gaza yin abubuwan da suka kamata.

Zaton da ‘yan Nijeriya suka yi wa Tinubu ba ya rasa nasaba da kokarinsa a lokacin da ya yi gwamnan Jihar Legas, kenan zai yi wahala ya gudanar da mulkinsa kamar na Buhari.

  • Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Dawo Da Tsohon Taken Nijeriya
  • Ranar Yara Ta Duniya: Inganta Rayuwar Yaran Nijeriya Shi Ne Abu Mafi Girma – Tinubu

Sai dai akasarin tsare-tsare da Tinubu ya zo da su sun kara sanya ‘yan Nijeriya cikin wahalhalu fiye da ba, inda har mutane masu rufin asiri wanda a baya suke dan lallaba rayuwarsu, wannan gwamnati ta tagayyara su sakamakon tsare-tsarenta.

ADVERTISEMENT

Idan aka duba matakinsa na farko a ranar 29 ga watan Mayun 2023, kamar yadda ya yi alkawari a lokacin yakin neman zabe, duk da yake dukkanin ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyun PDP da LP sun yi alkawarin janye tallafin mai idan sun sami nasara.

Tinubu ya ayyana janye tallafin mai kwata-kwata a jawabin amsar mulki da ya yi, inda ya nuna cewa za a yi amfani da kudaden da ake bayar da tallafin ne wajen zuba jari a bangaren gine-gine da ilimi da kula da lafiya da samar da ayyukan yi da kuma inganta rayuwar miliyoyin ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

Tun da aka janye tallafin mai fetur, farashin kayayyaki suka fara hauhawa ba kaukautawa, a cewar Tinubu da bai cire tallafin mai ba da yanzu kasar ta talauce.

A daidai lokacin da ‘yan Nijeriya suke fama da raunin janye tallafin mai, sai kuma gwamnatin Tinubu ta kawo wani tsari a kan darajar naira ko da yake wannan ma yana cikin alkawarin da ya yi a lokacin yakin neman zabe.

Gwamnati ta bayar da tallafi a matsayin rage radadin halin da mutane suke ciki, wanda za a iya cewa tallafin bai kai inda ya kamata ba, sannan gwamnati ta bayar da umurni a fitar da hatsi da rumbunanta a rarraba wa talakawa, amma mutane da dama ba su sami wannan tallafin ba, ko da yake wasu sun bayar da tabbacin cewa babu komai a wadannan rumbunan da gwamnati ta bayar da umurnin a bude a raba wa al’umma.

A bangaren gwamnati kuwa, kullum tana bai wa ‘yan Nijeriya uzurin cewa tana daukan wadannan matakai ne don inganta tattalin arzikin Nijeriya, kuma a cewarta nan ba da jimawa ‘yan Nijeriya za su dara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025
Tambarin Dimokuradiyya

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Next Post
Yawan Wutar Lantarki Da Jerin Madatsun Ruwa Dake Sin Suka Samar A Rubu’in Farko Na Bana Ya Zarce Kilowatts Biliyan 52

Yawan Wutar Lantarki Da Jerin Madatsun Ruwa Dake Sin Suka Samar A Rubu’in Farko Na Bana Ya Zarce Kilowatts Biliyan 52

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.