ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Daya Ta Mulki: Zaki Da Dacin Gwamnatin Tinubu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

A lokacin da Shugaba kasa, Bola Tinubu ya dare kan karagar mulkin Nijeriya, ‘yan Nijeriya da dama suka fara fatan ganin wahalhalun da suke ciki za su kau, musamman ganin cewa a wancan lokacin gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ta gaza yin abubuwan da suka kamata.

Zaton da ‘yan Nijeriya suka yi wa Tinubu ba ya rasa nasaba da kokarinsa a lokacin da ya yi gwamnan Jihar Legas, kenan zai yi wahala ya gudanar da mulkinsa kamar na Buhari.

  • Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Dawo Da Tsohon Taken Nijeriya
  • Ranar Yara Ta Duniya: Inganta Rayuwar Yaran Nijeriya Shi Ne Abu Mafi Girma – Tinubu

Sai dai akasarin tsare-tsare da Tinubu ya zo da su sun kara sanya ‘yan Nijeriya cikin wahalhalu fiye da ba, inda har mutane masu rufin asiri wanda a baya suke dan lallaba rayuwarsu, wannan gwamnati ta tagayyara su sakamakon tsare-tsarenta.

ADVERTISEMENT

Idan aka duba matakinsa na farko a ranar 29 ga watan Mayun 2023, kamar yadda ya yi alkawari a lokacin yakin neman zabe, duk da yake dukkanin ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyun PDP da LP sun yi alkawarin janye tallafin mai idan sun sami nasara.

Tinubu ya ayyana janye tallafin mai kwata-kwata a jawabin amsar mulki da ya yi, inda ya nuna cewa za a yi amfani da kudaden da ake bayar da tallafin ne wajen zuba jari a bangaren gine-gine da ilimi da kula da lafiya da samar da ayyukan yi da kuma inganta rayuwar miliyoyin ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Tun da aka janye tallafin mai fetur, farashin kayayyaki suka fara hauhawa ba kaukautawa, a cewar Tinubu da bai cire tallafin mai ba da yanzu kasar ta talauce.

A daidai lokacin da ‘yan Nijeriya suke fama da raunin janye tallafin mai, sai kuma gwamnatin Tinubu ta kawo wani tsari a kan darajar naira ko da yake wannan ma yana cikin alkawarin da ya yi a lokacin yakin neman zabe.

Gwamnati ta bayar da tallafi a matsayin rage radadin halin da mutane suke ciki, wanda za a iya cewa tallafin bai kai inda ya kamata ba, sannan gwamnati ta bayar da umurni a fitar da hatsi da rumbunanta a rarraba wa talakawa, amma mutane da dama ba su sami wannan tallafin ba, ko da yake wasu sun bayar da tabbacin cewa babu komai a wadannan rumbunan da gwamnati ta bayar da umurnin a bude a raba wa al’umma.

A bangaren gwamnati kuwa, kullum tana bai wa ‘yan Nijeriya uzurin cewa tana daukan wadannan matakai ne don inganta tattalin arzikin Nijeriya, kuma a cewarta nan ba da jimawa ‘yan Nijeriya za su dara.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Yawan Wutar Lantarki Da Jerin Madatsun Ruwa Dake Sin Suka Samar A Rubu’in Farko Na Bana Ya Zarce Kilowatts Biliyan 52

Yawan Wutar Lantarki Da Jerin Madatsun Ruwa Dake Sin Suka Samar A Rubu’in Farko Na Bana Ya Zarce Kilowatts Biliyan 52

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.