ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Daya Ta Mulki: Zaki Da Dacin Gwamnatin Tinubu

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

A lokacin da Shugaba kasa, Bola Tinubu ya dare kan karagar mulkin Nijeriya, ‘yan Nijeriya da dama suka fara fatan ganin wahalhalun da suke ciki za su kau, musamman ganin cewa a wancan lokacin gwamnatin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ta gaza yin abubuwan da suka kamata.

Zaton da ‘yan Nijeriya suka yi wa Tinubu ba ya rasa nasaba da kokarinsa a lokacin da ya yi gwamnan Jihar Legas, kenan zai yi wahala ya gudanar da mulkinsa kamar na Buhari.

  • Tinubu Ya Rattaba Hannu Kan Dokar Dawo Da Tsohon Taken Nijeriya
  • Ranar Yara Ta Duniya: Inganta Rayuwar Yaran Nijeriya Shi Ne Abu Mafi Girma – Tinubu

Sai dai akasarin tsare-tsare da Tinubu ya zo da su sun kara sanya ‘yan Nijeriya cikin wahalhalu fiye da ba, inda har mutane masu rufin asiri wanda a baya suke dan lallaba rayuwarsu, wannan gwamnati ta tagayyara su sakamakon tsare-tsarenta.

ADVERTISEMENT

Idan aka duba matakinsa na farko a ranar 29 ga watan Mayun 2023, kamar yadda ya yi alkawari a lokacin yakin neman zabe, duk da yake dukkanin ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyun PDP da LP sun yi alkawarin janye tallafin mai idan sun sami nasara.

Tinubu ya ayyana janye tallafin mai kwata-kwata a jawabin amsar mulki da ya yi, inda ya nuna cewa za a yi amfani da kudaden da ake bayar da tallafin ne wajen zuba jari a bangaren gine-gine da ilimi da kula da lafiya da samar da ayyukan yi da kuma inganta rayuwar miliyoyin ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Tun da aka janye tallafin mai fetur, farashin kayayyaki suka fara hauhawa ba kaukautawa, a cewar Tinubu da bai cire tallafin mai ba da yanzu kasar ta talauce.

A daidai lokacin da ‘yan Nijeriya suke fama da raunin janye tallafin mai, sai kuma gwamnatin Tinubu ta kawo wani tsari a kan darajar naira ko da yake wannan ma yana cikin alkawarin da ya yi a lokacin yakin neman zabe.

Gwamnati ta bayar da tallafi a matsayin rage radadin halin da mutane suke ciki, wanda za a iya cewa tallafin bai kai inda ya kamata ba, sannan gwamnati ta bayar da umurni a fitar da hatsi da rumbunanta a rarraba wa talakawa, amma mutane da dama ba su sami wannan tallafin ba, ko da yake wasu sun bayar da tabbacin cewa babu komai a wadannan rumbunan da gwamnati ta bayar da umurnin a bude a raba wa al’umma.

A bangaren gwamnati kuwa, kullum tana bai wa ‘yan Nijeriya uzurin cewa tana daukan wadannan matakai ne don inganta tattalin arzikin Nijeriya, kuma a cewarta nan ba da jimawa ‘yan Nijeriya za su dara.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
Yawan Wutar Lantarki Da Jerin Madatsun Ruwa Dake Sin Suka Samar A Rubu’in Farko Na Bana Ya Zarce Kilowatts Biliyan 52

Yawan Wutar Lantarki Da Jerin Madatsun Ruwa Dake Sin Suka Samar A Rubu’in Farko Na Bana Ya Zarce Kilowatts Biliyan 52

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.