• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Guda Bayan Zaben 2023: Har Yanzu Nijeriya Ba Ta Warware Ba

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Gwamnati Ta Dakatar Da Daraktocin Hukumar Sufurin Jiragen Sama 5 Sa’o’i Kadan Bayan Sauke Shugabanninsu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranakun 25 ga watan fabrairu da 11 ga watan Maris shekarar 2024, sun zama ranakun da suke tuna wa ‘yan Nijeriya lokacin da aka gudanar da zabuka masu cike da tarihi a kasar nan.

Wadannan ranakun ne da aka gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun kasa da kuma zaben gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi.

  • Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
  • Jimilar Kudin Da Sin Ta Samu Wajen Jigilar Kayayyaki A Farkon Watanni Biyu Na Bana Ta Kai Yuan Triliyan 55.4

Zabukan sun kasance masu muhimmancin gaske, kasancewar ana gudanar da gwamnatin farar hula na tsawon shekaru 24 ba tare da katse ba, ma’ana sojoji ba su amshi mulki ba, kuma karo na farko a tarihin Nijeriya tun bayan samun mulkin kai. An dai samu masu saka ido na cikin gida da kuma kasashen ketare da wadannan zabuka.

Mafi yawan masu sanya idanu sun bayyana cewa zaben 2023 shi ne mafi tsada a Nijeriya, inda ya lashe makudan kudade sama da naira biliyan 355 tun daga buga takardun jefa kuri’a har zuwa hidindimun da aka gudanar a lokacin zaben da kuma bayan zaben.

Duk da an sami karin rajistar masu zabe har miliyan 10 bayan a baya ana da miliyan 84, an sami karancin fitowar masu jefa kuri’a.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

A shekarun da suka gabata, an yi kokarin kauce wa wasu matslaolin zabe da ake samu kamar satar akwati da tarwatsa wajen zabe da wasu bata-gari ke yi da saye da sayar da kuri’a da matsalar tsaro da karya dokokin zabe da wasu jam’iyyu ke yi wajen tsayar da dan takara.

A batun gaskiya, zaben da aka gudanar a wasu yankuna a watan Nuwamba na shekarar 2023, ya sanya an gano wasu kura-kurai da jam’iyyun siyasa suke tafkawa, wanda ya zama izina ga hukuma da su kansu jam’iyyu. Hakan ta za aka dauki mataki a zaben gwamnonin da za a gudanar a jihohin Edo da Ondo a shekarar 2024.

Zaben 2023 ya zo da wasu kalubale da suka hada da fargaban rashin tsaro da matsalar tattalin arziki da talauci da ya addabi al’umma ta ko’ina, wanda ya hade da burukan ‘yan siyasa da suke neman madafun iko ta kowani hali.

Kafin lokacin zaben, wasu abubuwa sun kara bayyana kamar kabilanci da bangaranci da bambance-bambancen addini, wanda wadannan dalilai suna daga cikin abubuwan da suka sanya aka sami karancin masu fitowa zabe.

Haka kuma zaben 2023, an sayi kuri’u masu yawan gaske, inda ‘yan siyasa suka rika bai wa al’umma kudi da kyaututtuka, wadannan abubuwan sun shafi kima da darajar zaben matuka don sun yi tasiri sosai.

Baya ga wadannan kuma, wasu malaman addini da masana sun rika amfani da damarsu wajen kira da a zabi wasu bangare, wanda wannan ma ya saba wa tsarin dimokuradiyya. Amma a hannu guda kuma, wasu malaman da masana harkokin rayuwa sun taka muhimmiyar rawa wajen samun nasarar zaben 2023.

Hukumar INEC wacce a halin yanzu take shirin gudanar da zabukan gwamnoni a jihohin Edo da Ondo ba tare da an sami matsaloli ba kamar yadda aka samu a zaben gwamnonin jihohin Kogi da Imo da Bayelsa a kwanakin baya, ta ja hankalin jam’iyyun siyasa wajen ganin sun iya abun da ya dace bisa tsarin doka.

Sanin kowa ne a duk inda za a yi zabe a duniya ba wai a Njeriya ba, ba a rasa wasu matsaloli daga nan zuwa can. Amma a nan Nijeriya babban abun da ake bukata shi ne, hukumar INEC ta yi kokarin yin adalci wajen ayyukanta, yin haka ne kawai zai tabbatar da dorewar dimokuradiyya.

Sannan hakan ne zai sa al’umma su rika fitowa yin zaben, domin suna da tabbacin za a ba su abun da suka zaba, kuma za a tsare masu rayukansu.

Alamu dai na nuna cewa har yanzu dai a bangaren zabe, Nijeriya ba ta tsaya da kafafunta ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Katsewar Intanet: Samar Da Sabbin Wayoyi Zai Lakume Dala Biliyan 1

Next Post

Ya Kamata Gwamnati Ta Haramta Wa Mata Baza Jarirai A Titinan Kano – Sarkin Dillalan Kano

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

4 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

2 weeks ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

Ya Kamata Gwamnati Ta Haramta Wa Mata Baza Jarirai A Titinan Kano - Sarkin Dillalan Kano

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.