• English
  • Business News
Sunday, November 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shekara Guda Bayan Zaben 2023: Har Yanzu Nijeriya Ba Ta Warware Ba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Zabe

Ranakun 25 ga watan fabrairu da 11 ga watan Maris shekarar 2024, sun zama ranakun da suke tuna wa ‘yan Nijeriya lokacin da aka gudanar da zabuka masu cike da tarihi a kasar nan.

Wadannan ranakun ne da aka gudanar da zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun kasa da kuma zaben gwamnoni da na ‘yan majalisun jihohi.

  • Azumi Lokaci Zafi: Yadda ‘Yan Kasuwar Kankara Ke Camamarsu A Yobe Da Zamfara
  • Jimilar Kudin Da Sin Ta Samu Wajen Jigilar Kayayyaki A Farkon Watanni Biyu Na Bana Ta Kai Yuan Triliyan 55.4

Zabukan sun kasance masu muhimmancin gaske, kasancewar ana gudanar da gwamnatin farar hula na tsawon shekaru 24 ba tare da katse ba, ma’ana sojoji ba su amshi mulki ba, kuma karo na farko a tarihin Nijeriya tun bayan samun mulkin kai. An dai samu masu saka ido na cikin gida da kuma kasashen ketare da wadannan zabuka.

Mafi yawan masu sanya idanu sun bayyana cewa zaben 2023 shi ne mafi tsada a Nijeriya, inda ya lashe makudan kudade sama da naira biliyan 355 tun daga buga takardun jefa kuri’a har zuwa hidindimun da aka gudanar a lokacin zaben da kuma bayan zaben.

Duk da an sami karin rajistar masu zabe har miliyan 10 bayan a baya ana da miliyan 84, an sami karancin fitowar masu jefa kuri’a.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

A shekarun da suka gabata, an yi kokarin kauce wa wasu matslaolin zabe da ake samu kamar satar akwati da tarwatsa wajen zabe da wasu bata-gari ke yi da saye da sayar da kuri’a da matsalar tsaro da karya dokokin zabe da wasu jam’iyyu ke yi wajen tsayar da dan takara.

A batun gaskiya, zaben da aka gudanar a wasu yankuna a watan Nuwamba na shekarar 2023, ya sanya an gano wasu kura-kurai da jam’iyyun siyasa suke tafkawa, wanda ya zama izina ga hukuma da su kansu jam’iyyu. Hakan ta za aka dauki mataki a zaben gwamnonin da za a gudanar a jihohin Edo da Ondo a shekarar 2024.

Zaben 2023 ya zo da wasu kalubale da suka hada da fargaban rashin tsaro da matsalar tattalin arziki da talauci da ya addabi al’umma ta ko’ina, wanda ya hade da burukan ‘yan siyasa da suke neman madafun iko ta kowani hali.

Kafin lokacin zaben, wasu abubuwa sun kara bayyana kamar kabilanci da bangaranci da bambance-bambancen addini, wanda wadannan dalilai suna daga cikin abubuwan da suka sanya aka sami karancin masu fitowa zabe.

Haka kuma zaben 2023, an sayi kuri’u masu yawan gaske, inda ‘yan siyasa suka rika bai wa al’umma kudi da kyaututtuka, wadannan abubuwan sun shafi kima da darajar zaben matuka don sun yi tasiri sosai.

Baya ga wadannan kuma, wasu malaman addini da masana sun rika amfani da damarsu wajen kira da a zabi wasu bangare, wanda wannan ma ya saba wa tsarin dimokuradiyya. Amma a hannu guda kuma, wasu malaman da masana harkokin rayuwa sun taka muhimmiyar rawa wajen samun nasarar zaben 2023.

Hukumar INEC wacce a halin yanzu take shirin gudanar da zabukan gwamnoni a jihohin Edo da Ondo ba tare da an sami matsaloli ba kamar yadda aka samu a zaben gwamnonin jihohin Kogi da Imo da Bayelsa a kwanakin baya, ta ja hankalin jam’iyyun siyasa wajen ganin sun iya abun da ya dace bisa tsarin doka.

Sanin kowa ne a duk inda za a yi zabe a duniya ba wai a Njeriya ba, ba a rasa wasu matsaloli daga nan zuwa can. Amma a nan Nijeriya babban abun da ake bukata shi ne, hukumar INEC ta yi kokarin yin adalci wajen ayyukanta, yin haka ne kawai zai tabbatar da dorewar dimokuradiyya.

Sannan hakan ne zai sa al’umma su rika fitowa yin zaben, domin suna da tabbacin za a ba su abun da suka zaba, kuma za a tsare masu rayukansu.

Alamu dai na nuna cewa har yanzu dai a bangaren zabe, Nijeriya ba ta tsaya da kafafunta ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

Ya Kamata Gwamnati Ta Haramta Wa Mata Baza Jarirai A Titinan Kano - Sarkin Dillalan Kano

LABARAI MASU NASABA

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

November 2, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Maganin Nankarwa (3)

Maganin Nankarwa (3)

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legas

November 2, 2025
Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka

November 2, 2025
Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

November 2, 2025
Yaya Da Kani Sun Mutu A Cikin Ramin Masai A Kano

An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano

November 2, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.