• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
1 year ago
in Wasanni
0
Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta fara kakar wasa ta bana tare da sabon gogaggen dan wasa cikin jerin sunayen ƴan wasansu bayan da suka kara Kylian Mbappé a cikin tawagar kungiyar sai dai kuma hakan bai sa kungiyar ta samu nasara ba a wasanta na farko da Real Mallorca.

 

Real Madrid za ta nemi maimaita nasarar da ta samu a kakar wasan da ta gabata inda kungiyar ta lashe gasar La Liga da kuma Champions League kuma an ga anfanin hakan bayan nasara a kan Atalanta da ci 2-0, inda ta lashe kofin Uefa super cup, kuma Mbappe ya ci wa kungiyar kwallonsa na farko.

  • Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA
  • An Samar Da Naira Biliyan 2.5 Don Bunkasa Ma’adanai A Nijeriya

Zakarun na nahiyar turai sun kara wa tawagarta karfi da ƴan wasa biyu a wannan bazarar bayan ta kammala daukar Kyllian Mbappé daga Paris Saint-Germain da kuma Endrick Felipe daga Palmeiras ta Brazil.

 

Labarai Masu Nasaba

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Amma har yanzu wasu suna ganin Real Madrid za ta sha wahala a wannan kakar saboda ritayar da dan wasa Toni Kroos ya yi a karshen kakar da ta gabata bayan ya taimaka wa kungiyar ta lashe gasar cin kofin zakarun turai a watan Yuni.

 

Toni Kroos ya rataye takalman wasansa ya kuma bar Ancelotti da babban gibi a tsakiya. Haka kuma kyaftin Nacho, wanda ya bar kungiyar zuwa Al-Kadisiyah, sai kuma dan wasan gaba Joselu, wanda ya koma kungiyar Al-Gharafa ta kasar Katar.

 

Sai dai ganin yadda sauran kungoyoyin La Liga ke shirin tunkarar kakar wasan bana, ba abin mamaki ba ne idan kungiyoyin Barcelona da Atletico Madrid suka takawa kungiyar burki wajen lashe gasar Laliga ta bana.

 

Barcelona – wadda ita ce babbar abokiyar hamayyar Real Madrid ana ganin akwai alamun rauni ganin yadda ta shiga rudani a kasuwar cinikin ‘ƴan wasa na bazarar nan, inda ya zuwa yanzu take kai wa da kawowa wurin neman ƴan wasan da za ta dauko domin kara wa tawagarta karfi.

 

A yanzu ɗan wasa mai armashi daya tilo da Barca da dauka shi ne Dani Olmo, duk da daukar lokaci da aka yi ana danganta kungiyar da dan wasan kungiyar Athletico Bilbao, Nico Williams, wanda ya taimaka wa Spaniya ta lashe kofin nahiyar turai a Jamus.

 

Ita kuwa Atlético Madrid ta yi manyan sauye-sauye a tawagarta inda ta sallami Albaro Morata ta kuma maye gurbinsa da Julian Albarez daga manchester City sai kuma dan wasa Conor Gallagher da kungiyar ta dauka daga Chelsea.

 

Ita kuma Girona da ta samu tagomashi a bara ta sallami ‘ƴan wasanta da dama da suka taka mata rawar gani a kakar wasan amma kungiyar ta dauki Donny Ban de Beek daga Manchester United da wasu ‘yan wasan a Spaniya.

 

A Real Madrid, a bangaren mai tsaron raga, Thibaut Courtois ya taka rawar gani a wasannin share fage na wannan bazarar tunda bai je gasar nahiyar turai ba da Belgium, duk da kokarin da Andriy Lunin ya yi a bara, ana sa ran dan wasan na Belgium zai kasance zabin farko na Carlo Ancelotti.

 

A masu tsaron baya, tafiyar Nacho na nufin cewa Éder Militão na shirin komawa matsayinsa na mai tsaron baya na tsakiya tare da Antonio Rüdiger amma ana ganin akwai bukatar kungiyar ta sayi wani dan wasan bayan ta kara. Amma kungiyar ta so daukar Leny Yoro, wanda ya koma Manchester United.

 

Yin ritayarToni Kroos ta bar babban gibi amma ana ganin wanda zai ci gajiyar hakan shi ne Eduardo Camabinga, wanda ya samu damar buga wasanni da dama a kakar wasan da ta gabata, kodayake Luka Modrić shi ma zai taka muhimmiyar rawa sakamakon gogewar da yake da ita wanda zai taimaka matuka a wasu wasannin.

 

Zuwan Kylian Mbappé na nufin cewa dole ne kociyan kungiyar Carlo Ancelotti yasan yadda za a yi a yi wa dan wasan waje saboda ana ganin Rodrygo Goes zai iya komawa benci, idan aka yi duba da irin hazakar Binícius Júnior da Jude Bellingham.

 

Duk da haka ana ganin mai tsaron raga Andriy Lunin zai iya ficewa daga kungiyar domin neman gurbin buga wasa a wata kungiya, wanda hakan ka iya bude kofa ga yuwuwar dawowar dan wasan aro na bara, Kepa Arrizabalaga daga Chelsea.

 

Amma kuma duk da haka ana ganin Barcelona da Atletico Madrid ba za su yi kara a gwiwa ba wajen ganin sun lashe gasar ta bana saboda wasan farko ma da Real Madrid ta buga canjaras ta buga, wanda hakan yake nuna cewa akwai babban aiki a gaban kociyan kungiyar, Carlo Ancelotti.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Su Wa Ke Da Hannu Wajen Badakalar Yaye Daliban Bogi A Jami’ar Kalaba?

Next Post

Kasar Sin Ta Kara Ware Kudaden Agajin Gaggawa Ga Lardin Liaoning Dake Arewa Maso Gabashin Kasar

Related

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack
Wasanni

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

2 days ago
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 
Wasanni

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

5 days ago
Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein
Wasanni

Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

5 days ago
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana
Wasanni

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

7 days ago
Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana
Wasanni

Ƴan Wasan Nijeriya Da Suka Sauya Sheka A Kasuwar Musayar Ƴan Ƙwallo Ta Bana

7 days ago
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda
Wasanni

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

1 week ago
Next Post
Kasar Sin Ta Kara Ware Kudaden Agajin Gaggawa Ga Lardin Liaoning Dake Arewa Maso Gabashin Kasar

Kasar Sin Ta Kara Ware Kudaden Agajin Gaggawa Ga Lardin Liaoning Dake Arewa Maso Gabashin Kasar

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.