ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Barcelona Da Atletico Madrid Zu Su Iya Dakatar Da Real Madrid A La Liga?

by Abba Ibrahim Wada and Sulaiman
2 years ago
Madrid

Kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta fara kakar wasa ta bana tare da sabon gogaggen dan wasa cikin jerin sunayen ƴan wasansu bayan da suka kara Kylian Mbappé a cikin tawagar kungiyar sai dai kuma hakan bai sa kungiyar ta samu nasara ba a wasanta na farko da Real Mallorca.

 

Real Madrid za ta nemi maimaita nasarar da ta samu a kakar wasan da ta gabata inda kungiyar ta lashe gasar La Liga da kuma Champions League kuma an ga anfanin hakan bayan nasara a kan Atalanta da ci 2-0, inda ta lashe kofin Uefa super cup, kuma Mbappe ya ci wa kungiyar kwallonsa na farko.

ADVERTISEMENT
  • Mutum Miliyan 7.9 Da Ta’addanci Ya Tagayyara A Jihohi 3 Na Bukatar Agaji – UNOCHA
  • An Samar Da Naira Biliyan 2.5 Don Bunkasa Ma’adanai A Nijeriya

Zakarun na nahiyar turai sun kara wa tawagarta karfi da ƴan wasa biyu a wannan bazarar bayan ta kammala daukar Kyllian Mbappé daga Paris Saint-Germain da kuma Endrick Felipe daga Palmeiras ta Brazil.

 

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Amma har yanzu wasu suna ganin Real Madrid za ta sha wahala a wannan kakar saboda ritayar da dan wasa Toni Kroos ya yi a karshen kakar da ta gabata bayan ya taimaka wa kungiyar ta lashe gasar cin kofin zakarun turai a watan Yuni.

 

Toni Kroos ya rataye takalman wasansa ya kuma bar Ancelotti da babban gibi a tsakiya. Haka kuma kyaftin Nacho, wanda ya bar kungiyar zuwa Al-Kadisiyah, sai kuma dan wasan gaba Joselu, wanda ya koma kungiyar Al-Gharafa ta kasar Katar.

 

Sai dai ganin yadda sauran kungoyoyin La Liga ke shirin tunkarar kakar wasan bana, ba abin mamaki ba ne idan kungiyoyin Barcelona da Atletico Madrid suka takawa kungiyar burki wajen lashe gasar Laliga ta bana.

 

Barcelona – wadda ita ce babbar abokiyar hamayyar Real Madrid ana ganin akwai alamun rauni ganin yadda ta shiga rudani a kasuwar cinikin ‘ƴan wasa na bazarar nan, inda ya zuwa yanzu take kai wa da kawowa wurin neman ƴan wasan da za ta dauko domin kara wa tawagarta karfi.

 

A yanzu ɗan wasa mai armashi daya tilo da Barca da dauka shi ne Dani Olmo, duk da daukar lokaci da aka yi ana danganta kungiyar da dan wasan kungiyar Athletico Bilbao, Nico Williams, wanda ya taimaka wa Spaniya ta lashe kofin nahiyar turai a Jamus.

 

Ita kuwa Atlético Madrid ta yi manyan sauye-sauye a tawagarta inda ta sallami Albaro Morata ta kuma maye gurbinsa da Julian Albarez daga manchester City sai kuma dan wasa Conor Gallagher da kungiyar ta dauka daga Chelsea.

 

Ita kuma Girona da ta samu tagomashi a bara ta sallami ‘ƴan wasanta da dama da suka taka mata rawar gani a kakar wasan amma kungiyar ta dauki Donny Ban de Beek daga Manchester United da wasu ‘yan wasan a Spaniya.

 

A Real Madrid, a bangaren mai tsaron raga, Thibaut Courtois ya taka rawar gani a wasannin share fage na wannan bazarar tunda bai je gasar nahiyar turai ba da Belgium, duk da kokarin da Andriy Lunin ya yi a bara, ana sa ran dan wasan na Belgium zai kasance zabin farko na Carlo Ancelotti.

 

A masu tsaron baya, tafiyar Nacho na nufin cewa Éder Militão na shirin komawa matsayinsa na mai tsaron baya na tsakiya tare da Antonio Rüdiger amma ana ganin akwai bukatar kungiyar ta sayi wani dan wasan bayan ta kara. Amma kungiyar ta so daukar Leny Yoro, wanda ya koma Manchester United.

 

Yin ritayarToni Kroos ta bar babban gibi amma ana ganin wanda zai ci gajiyar hakan shi ne Eduardo Camabinga, wanda ya samu damar buga wasanni da dama a kakar wasan da ta gabata, kodayake Luka Modrić shi ma zai taka muhimmiyar rawa sakamakon gogewar da yake da ita wanda zai taimaka matuka a wasu wasannin.

 

Zuwan Kylian Mbappé na nufin cewa dole ne kociyan kungiyar Carlo Ancelotti yasan yadda za a yi a yi wa dan wasan waje saboda ana ganin Rodrygo Goes zai iya komawa benci, idan aka yi duba da irin hazakar Binícius Júnior da Jude Bellingham.

 

Duk da haka ana ganin mai tsaron raga Andriy Lunin zai iya ficewa daga kungiyar domin neman gurbin buga wasa a wata kungiya, wanda hakan ka iya bude kofa ga yuwuwar dawowar dan wasan aro na bara, Kepa Arrizabalaga daga Chelsea.

 

Amma kuma duk da haka ana ganin Barcelona da Atletico Madrid ba za su yi kara a gwiwa ba wajen ganin sun lashe gasar ta bana saboda wasan farko ma da Real Madrid ta buga canjaras ta buga, wanda hakan yake nuna cewa akwai babban aiki a gaban kociyan kungiyar, Carlo Ancelotti.

Madrid
Abba Ibrahim Wada
Website |  + posts Bio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City
Madrid
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Kara Ware Kudaden Agajin Gaggawa Ga Lardin Liaoning Dake Arewa Maso Gabashin Kasar

Kasar Sin Ta Kara Ware Kudaden Agajin Gaggawa Ga Lardin Liaoning Dake Arewa Maso Gabashin Kasar

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.