• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Batun Kare Hakkin Bil Adama Makami Ne Kawai Na Dakile Ci Gaban Wasu Kasashe?

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Shin Batun Kare Hakkin Bil Adama Makami Ne Kawai Na Dakile Ci Gaban Wasu Kasashe?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Rikici tsakanin Isra’ila da Palasdinu ba sabon abu ba ne ga al’ummar kasa da kasa, amma kuma abu ne na tayar da hankali ganin yadda ake ta gadon rikicin daga zuri’a zuwa zuri’a tamkar wata al’adar gargajiya. Rikici da mace-mace batu ne da bai kamata duniya ta lamunta ba, haka kuma batu ne dake bukatar a lalubo bakin zaren warware shi tun daga tushe.

A ranar Lahadi, ofishin manyan jami’an MDD mai kula da hakkokin bil adama ya ce yanayin keta hakkin bil adama a Zirin Gaza na kara tsananta, yana mai cewa matakin Isra’ila sun sabawa dokar kare hakkin bil adama ta kasa da kasa. Sai dai maimakon a ji kasashen duniya dake ganin kansu a matsayin manya kuma masu fada a ji suna daga murya game da hakan, shiru ka ake ji, sai ma kokarin da suke yi ta kowacce hanya na karawa mai cin zali karfi wajen ci gaba da aikata mummunan aikin da galibin kasashen duniya ke tir da shi. Yadda ake yayata batun kare hakkin bil adama a baki, ya bambanta da aiwatar da shi a aikace. Mun ga yadda ake matsawa kasa kamar Sin a kokarinta na tabbatar da zaman lafiya a yankunanta, inda ake ta kakkaba takunkumai da bata mata suna bisa hujjar hakkin bil adama, amma aka gaza daukar matakin da ya dace kan wadanda kowa ya yi amana cewa, suna keta wannan hakki. Shin kare hakkin bil da ake yayatawa makami ne kawai na dakile kasashen dake samun ci gaba da kokarin tabbatar da zaman lafiya, maimakon kare ainihin wadanda ke bukatar kariya?

A jiya Litinin, kasar Sin ta yi kira da kasashe masu ruwa da tsaki kada su kawo cikas ga batun kasancewar Palasdinu mamba a MDD, kuma kada su ci gaba da adawa da burin kasa da kasa, ganin yadda wadannan kasashe suke hawan kujerar naki kan wannan batu. Ba sau daya ba, kasashen duniya sun bayyana burinsu na ganin an samar da zaman lafiya da tabbatar da halaltattun hakkokin Palasdinawa, amma kuma wasu kasashe na yi wa wannan buri kafar ungulu. Kasar Sin na daya daga cikin kasashen da suka dauki nauyin gabatar da kudurin kasancewar Palasdinu cikakkiyar mamba a MDD da kuma wadanda suka kada kuri’ar amincewa da shi da sauran kudurorin da suka shafi kare hakkokin Palasdinawa da tabbatar da zaman lafiya a yankin, kamar yadda ya kamata kowace kasa dake kaunar zaman lafiya ta yi. Sai dai da alama wasu kasashe ba sa burin ganin kawo karshen wannan rikici da ma wanzuwar zaman lafiya a duniya. Kana kalaman da su kan furta na rajin kare hakkin bil adama, ya bambanta da abun da suke aiwatarwa a zahiri. Rikicin Palasdinu da Isra’ila ya kara tabbatarwa duniya wannan da kuma irin fuskoki biyu da ake nunawa a al’amuran da suka shafi kare fararen hula masu rauni. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JapanSinTaiwan
ShareTweetSendShare
Previous Post

Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Next Post

Hajjin Bana: Ranar 23 Ga Watan Mayu Za A Fara Jigilar Maniyyatan Jihar Kaduna – Hukuma

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

42 minutes ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

2 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

3 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

4 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

5 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

24 hours ago
Next Post
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin Bana: Ranar 23 Ga Watan Mayu Za A Fara Jigilar Maniyyatan Jihar Kaduna - Hukuma

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.