ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Batun Kare Hakkin Bil Adama Makami Ne Kawai Na Dakile Ci Gaban Wasu Kasashe?

by CGTN Hausa
2 years ago
Bil Adama

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Rikici tsakanin Isra’ila da Palasdinu ba sabon abu ba ne ga al’ummar kasa da kasa, amma kuma abu ne na tayar da hankali ganin yadda ake ta gadon rikicin daga zuri’a zuwa zuri’a tamkar wata al’adar gargajiya. Rikici da mace-mace batu ne da bai kamata duniya ta lamunta ba, haka kuma batu ne dake bukatar a lalubo bakin zaren warware shi tun daga tushe.

A ranar Lahadi, ofishin manyan jami’an MDD mai kula da hakkokin bil adama ya ce yanayin keta hakkin bil adama a Zirin Gaza na kara tsananta, yana mai cewa matakin Isra’ila sun sabawa dokar kare hakkin bil adama ta kasa da kasa. Sai dai maimakon a ji kasashen duniya dake ganin kansu a matsayin manya kuma masu fada a ji suna daga murya game da hakan, shiru ka ake ji, sai ma kokarin da suke yi ta kowacce hanya na karawa mai cin zali karfi wajen ci gaba da aikata mummunan aikin da galibin kasashen duniya ke tir da shi. Yadda ake yayata batun kare hakkin bil adama a baki, ya bambanta da aiwatar da shi a aikace. Mun ga yadda ake matsawa kasa kamar Sin a kokarinta na tabbatar da zaman lafiya a yankunanta, inda ake ta kakkaba takunkumai da bata mata suna bisa hujjar hakkin bil adama, amma aka gaza daukar matakin da ya dace kan wadanda kowa ya yi amana cewa, suna keta wannan hakki. Shin kare hakkin bil da ake yayatawa makami ne kawai na dakile kasashen dake samun ci gaba da kokarin tabbatar da zaman lafiya, maimakon kare ainihin wadanda ke bukatar kariya?

A jiya Litinin, kasar Sin ta yi kira da kasashe masu ruwa da tsaki kada su kawo cikas ga batun kasancewar Palasdinu mamba a MDD, kuma kada su ci gaba da adawa da burin kasa da kasa, ganin yadda wadannan kasashe suke hawan kujerar naki kan wannan batu. Ba sau daya ba, kasashen duniya sun bayyana burinsu na ganin an samar da zaman lafiya da tabbatar da halaltattun hakkokin Palasdinawa, amma kuma wasu kasashe na yi wa wannan buri kafar ungulu. Kasar Sin na daya daga cikin kasashen da suka dauki nauyin gabatar da kudurin kasancewar Palasdinu cikakkiyar mamba a MDD da kuma wadanda suka kada kuri’ar amincewa da shi da sauran kudurorin da suka shafi kare hakkokin Palasdinawa da tabbatar da zaman lafiya a yankin, kamar yadda ya kamata kowace kasa dake kaunar zaman lafiya ta yi. Sai dai da alama wasu kasashe ba sa burin ganin kawo karshen wannan rikici da ma wanzuwar zaman lafiya a duniya. Kana kalaman da su kan furta na rajin kare hakkin bil adama, ya bambanta da abun da suke aiwatarwa a zahiri. Rikicin Palasdinu da Isra’ila ya kara tabbatarwa duniya wannan da kuma irin fuskoki biyu da ake nunawa a al’amuran da suka shafi kare fararen hula masu rauni. (Fa’iza Mustapha)

ADVERTISEMENT
Bil Adama
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin Bana: Ranar 23 Ga Watan Mayu Za A Fara Jigilar Maniyyatan Jihar Kaduna - Hukuma

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.