ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Batun Kare Hakkin Bil Adama Makami Ne Kawai Na Dakile Ci Gaban Wasu Kasashe?

by CGTN Hausa
2 years ago
Bil Adama

LABARAI MASU NASABA

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Rikici tsakanin Isra’ila da Palasdinu ba sabon abu ba ne ga al’ummar kasa da kasa, amma kuma abu ne na tayar da hankali ganin yadda ake ta gadon rikicin daga zuri’a zuwa zuri’a tamkar wata al’adar gargajiya. Rikici da mace-mace batu ne da bai kamata duniya ta lamunta ba, haka kuma batu ne dake bukatar a lalubo bakin zaren warware shi tun daga tushe.

A ranar Lahadi, ofishin manyan jami’an MDD mai kula da hakkokin bil adama ya ce yanayin keta hakkin bil adama a Zirin Gaza na kara tsananta, yana mai cewa matakin Isra’ila sun sabawa dokar kare hakkin bil adama ta kasa da kasa. Sai dai maimakon a ji kasashen duniya dake ganin kansu a matsayin manya kuma masu fada a ji suna daga murya game da hakan, shiru ka ake ji, sai ma kokarin da suke yi ta kowacce hanya na karawa mai cin zali karfi wajen ci gaba da aikata mummunan aikin da galibin kasashen duniya ke tir da shi. Yadda ake yayata batun kare hakkin bil adama a baki, ya bambanta da aiwatar da shi a aikace. Mun ga yadda ake matsawa kasa kamar Sin a kokarinta na tabbatar da zaman lafiya a yankunanta, inda ake ta kakkaba takunkumai da bata mata suna bisa hujjar hakkin bil adama, amma aka gaza daukar matakin da ya dace kan wadanda kowa ya yi amana cewa, suna keta wannan hakki. Shin kare hakkin bil da ake yayatawa makami ne kawai na dakile kasashen dake samun ci gaba da kokarin tabbatar da zaman lafiya, maimakon kare ainihin wadanda ke bukatar kariya?

A jiya Litinin, kasar Sin ta yi kira da kasashe masu ruwa da tsaki kada su kawo cikas ga batun kasancewar Palasdinu mamba a MDD, kuma kada su ci gaba da adawa da burin kasa da kasa, ganin yadda wadannan kasashe suke hawan kujerar naki kan wannan batu. Ba sau daya ba, kasashen duniya sun bayyana burinsu na ganin an samar da zaman lafiya da tabbatar da halaltattun hakkokin Palasdinawa, amma kuma wasu kasashe na yi wa wannan buri kafar ungulu. Kasar Sin na daya daga cikin kasashen da suka dauki nauyin gabatar da kudurin kasancewar Palasdinu cikakkiyar mamba a MDD da kuma wadanda suka kada kuri’ar amincewa da shi da sauran kudurorin da suka shafi kare hakkokin Palasdinawa da tabbatar da zaman lafiya a yankin, kamar yadda ya kamata kowace kasa dake kaunar zaman lafiya ta yi. Sai dai da alama wasu kasashe ba sa burin ganin kawo karshen wannan rikici da ma wanzuwar zaman lafiya a duniya. Kana kalaman da su kan furta na rajin kare hakkin bil adama, ya bambanta da abun da suke aiwatarwa a zahiri. Rikicin Palasdinu da Isra’ila ya kara tabbatarwa duniya wannan da kuma irin fuskoki biyu da ake nunawa a al’amuran da suka shafi kare fararen hula masu rauni. (Fa’iza Mustapha)

ADVERTISEMENT
Bil Adama
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

MASU ALAKA

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina
Daga Birnin Sin

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta
Daga Birnin Sin

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
Next Post
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin Bana: Ranar 23 Ga Watan Mayu Za A Fara Jigilar Maniyyatan Jihar Kaduna - Hukuma

LABARAI MASU NASABA

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026
Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Gwamna Yusuf Ya Naɗa Muhuyi A Matsayin Shugaban Kwamitin Yaƙi Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano

June 25, 2026
Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

Wani Gidan Adana Kayan Tarihi Na Sin Ya Fitar Da Rahoton Yadda Dakarun Japan Suka Rika Zubawa Mutane Jinin Dabbobi Yayin Yakin Duniya Na Biyu

June 25, 2026
Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

Wang Yi Ya Yi Kira Da A Gaggauta Bude Mashigin Hormuz

June 25, 2026
Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

Ƙungiyar NPCF Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Ga Tinubu

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.