• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shin Wane Ne Kashim Shettima?

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Siyasa
0
Kashim Shettima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata Kashim Shettima mutum ne mai matukar basira, kuma kwararre, kana dan siyasa ne wanda ya lakanci magana a lokacin da ya dace cike da fasaha, wanda kuma dan asalin kabilar Kanuri ne.

Sanata Shettima mutum ne wanda aka sanshi da iya mu’amala, yana da raha kuma ba ya fushi, sannan ba ya nuna kyama da wariya ga kowane bangare.

  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Umarnin Sayar Da Takin Noma Miliyan 1.7 Ga Manoman Jihar

A lokacin da Kashim Shettima yake gwamnan jihar Borno (2011-2019) domin tabbatar da rashin nuna wariya da hadin-kan kasa, ya yi bajintar jawo kowane bangare a mulkinsa, wanda ya dauki mataimaka masu ba shi shawara wanda ya hada da dan kabilar Ibo kuma Kirista daga jihar Anambra, daya dan kabilar Urhobo Kirista daga jihar Delta, hadi da daya Kirista dan asalin jihar Edo, daya Bayarabe shima Kirista, sannan da daya Bafulatani daga jihar Gombe tare da daya Bahaushe daga jihar Zamfara.

An haifi Sanata Kashim Shettima, tsohon gwamnan jihar Borno ranar 2 ga watan Satumban 1966 a birnin Maiduguri, ta jihar Borno, da ke Arewa Maso Gabashin Nijeriya, wanda ya fito ne daga zuriyar marigayi Sir Kashim Ibrahim. Wanda daga bisani ya auri matarsa, Uwargida Nana Shettima, suna da ‘ya’ya uku, mata biyu da namiji daya.

Sanata Shettima ya fara karatun sa na firamari a Lamisula Primary School dake Maiduguri a 1972 zuwa 1978; sai Gobernment Community Secondary School, dake garin Biu a kudancin jihar tsakanin 1978 zuwa 1980; wanda daga bisani aka koma Gobernment Science Secondary School, Potiskum a jihar Yobe (makobciyar jihar Borno) wanda nan ya kammala karatun sa na sakandire a 1983. Sanata Kashim ya tafi Jami’ar Maiduguri inda ya yi digirinsa (BSc) kan Agricultural Economics a 1989. Sannan da aikin yiwa kasa hidima (NYSC) a Bankin ‘Nigerian Agricultural Cooperatibe Bank’, a Calabar na jihar Cross Riber a 1989-1990.

Labarai Masu Nasaba

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

Haka zalika, ya samu digirinsa na biyu (MSc) kan Agricultural Economics a 1991, a Jami’ar Ibadan. Sannan daga baya Shettima ya fara aikin Malanta a Jami’ar Maiduguri a tsangayar Agricultural Economics tsakanin 1991 zuwa 1993.

A shekarar 1993, Kashim ya mazaya zuwa aikin banki, inda ya fara aiki da rusasshen bankin ‘Commercial Bank of Africa Limited’ a matsayin babban akanta zuwa Manajan Bankin, a cibiyar bankin da ke unguwar Ikeja, a jihar Lagos.

A shekarar 2001, Shettima ya kowa aiki da Zenith Bank a matsayin shugaban reshen bankin a Maiduguri, kuma ya rike Babban manaja a bankin zuwa mataimakin Janar Manajan yankin Arewa Maso Gabas kafin daga bisani ya ajiye mukamin sa na Janar Manajan Bankin a 2007, sakamakon nada shi Kwamishinan kudi da ci gaban tattalin arziki na jihar Borno, kana kuma ya rike mukamin Kwamishina a ma’aikatu 5; a ma’aikatar kananan hukumomi da harkokin masarautu, na ma’aikatar ilimi, na ma’aikatar aikin gona tare da na ma’aikatar kiyon lafiya a lokacin tsohon Gwamnan jihar, Sanata Ali Modu Sheriff.

A zaben fid-da-gwanin jam’iyyar ANPP na watan Junairun 2011, an zabi Engineer Modu Fannami Gubio a matsayin dan takarar Gwamnan jihar Borno, wanda daga bisani wasu mahara suka kashe shi, a sa’ilin da Shettima shi ne ya zo na biyu a zaben fid-da-gwanin tare da maye-gurbinsa da marigayin. A zaben 26 ga April 2011, Kashim Shettima ya lashe zaben da kuri’u 531,147 wanda ya kayar da abokin hamayyarsa na jam’iyyar PDP, Muhammed Goni, da kuri’u 450,140.

Sanata Kashim ya sake lashe zaben gwamnan jihar a 2015 a karkashin jam’iyyar APC, yayin da kuma aka zabe shi matsayin shugaban kungiyar gwamnonin Arewacin Nijeriya 19. Wanda ya yi amfani da wannan dama ta jan akalar kungiyar gwamnonin wajen samar da hadin kan Arewacin Nijeriya hadi da yunkurin sake farfado da masana’antun da yankin ya mallaka wadanda ke fuskantar barazanar durkushewa.

Duk da irin kalubalen da jihar Borno ta fuskanta sakamakon tabarbarewar tsaron da kungiyar Boko Haram ya haifar wanda ya fara a 2011, gwamna Kashim Shettima ya taka rawar gani wajen gudanar da mulkin jihar. Yayin da Mai Baiwa Shugaban Kasa shawara ta fuskar tsaro da Hafsan Sojojin Nijeriya duk yan asalin jihar ne, kana da irin yadda gwamnatin tarayya ta sahale masa damar daukar matasa Yan Cibilian JTF a 2013.

Aikin sa-kai na Yan Cibilian JTF ya taimaka ainun wajen taimakon Sojojin Nijeriya a yakin da suke yi da mayakan kungiyar Boko Haram. Al’amarin da ya dada karsashin gwamnatin Shettima wajen saya wa yan cibilian JTF motoci da kayan yaki, kayan alatu da alawus a kokarin da suka nuna wajen goyon bayan sojojin.

Sanata Kashim Shettima ya taka muhimmiyar rawa wajen bayar da cikakken goyon baya ga Sojojin Nijeriya hadi da sauran jami’in tsaro a lokacin yaki da matsalar tsaro Boko Haram, wanda idan ba a manta ba, a September 2014, tabarbarewar tsaron ta yi kamari a birnin Maiduguri, da jihar Borno baki daya inda mayakan suka mamaye kananan hukumomi 20 a cikin 27 a jihar, al’amarin da ya tilasta wa jama’a kauracewa garuruwansu da jihar baki daya; kafin daga bisani Sojojin Nijeriya su fatattake su tsakanin 2015-2016. Amma domin bai wa jama’a kwarin gwiwa, a tsakiyar wannan halin, Gwamna Kashim Shettima ya dawo Maiduguri tare da gangami na musamman domin kare martabar jihar.

Bugu da kari kuma, gwamna Kashim Shettima ya daura damarar inganta rayuwar al’ummar da rikicin Boki Haram ya rutsa da su ta hanyar samar muhallin wucin-gadi da gyara wadansu domin tsugunnar da jama’a. Wanda daga baya gwamnatin sa ta fito da ingantaccen shiri na musamman domin sake farfado da yankunan da rikicin ya shafa a jihar, yayin da aka samu gagarumar nasara tare da sake tsugunnar da jama’a. Haka kuma Kashim Shettima ya dukufa wajen sauya fasalin harkokin ilimi tare da bunkasa makarantun firamari da sakandire a jihar hadi da na kwana domin bai wa marayu kimanin 50, 000 wadanda suka rasa mahaifa sakamakon matsalar tsaro a fadin jihar.

Biyo bayan jajircewa da kwazon gwamna Kashim Shettima ya jawo masa tagomashi da mambobin yabo a ciki da wajen Nijeriya. A 2014 ne Gwamna Shettima ya lashe kambin gwarzon gwamna na shekara a kamfanin Jaridar Leadership, Gwarzon Gwamna Na Shekarar 2015, na Uwar Kungiyar Yan Jaridu ta kasa (NUJ); Gwarzon Gwamnan Shekarar 2015 na NewsWatchTimes Newspapers, Gwarzon Gwamnan Shekarar 2015 na Jaridar Banguard Newspapers; Gwarzon Gwamnan Shekarar 2016 na Mujjalar Tell Magazine kuma wanda ya lashe kautar lambar yabo ta 2017 (Zik Prize) ga shugabani; kana da lambar yabo ta ‘Kaduna NUJ Award’ ta 2017, da FCT NUJ Merit Award a 2017.

Har wala yau, kafin ayyana shi a matsayin Mataimakin dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, wanda Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya yi a wannan makon, Sanata Kashim Shettima shi ne Sanata mai wakilatar jihar Borno ta tsakiyar a majalisar dattawan Nijeriya, a zaben 2019 da ya gabata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Nada Kashim Mataimakin Tinubu Ya Dumama Siyasar Nijeriya

Next Post

‘Gaskiyar Abin Da Ya Sa Sarkin Kano Bai Kai Gaisuwar Sallah Fadar Gwamnati Ba’

Related

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

2 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

2 days ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

2 days ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

4 days ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

5 days ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

6 days ago
Next Post
Kano

‘Gaskiyar Abin Da Ya Sa Sarkin Kano Bai Kai Gaisuwar Sallah Fadar Gwamnati Ba’

LABARAI MASU NASABA

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.