• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Bunƙasa Ilmi A Kano: Yadda Gwamnatin Abba Gida-gida Ta Tura Dalibai 1001 Karatu Kasashen Waje

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Shirin Bunƙasa Ilmi A Kano: Yadda Gwamnatin Abba Gida-gida Ta Tura Dalibai 1001 Karatu Kasashen Waje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ƙoƙarin ta daukaka darajar ilmi, Gwamnatin Jihar Kano ta zaɓi ɗalibai 1001 da ta fara ɗaukar nauyin karatunsu a digiri na biyu a ƙasashen waje.

An rahoto cewa, daga cikin Daliban akwai wadanda aka tura zuwa Jami’o’in kasar Indiya wasu kuma zuwa Jami’o’in Kasar Uganda domin samun ilimi a fanni daban-daban.

  • Dage Takunkumin CBN A Asusun Ajiyar Wasu Mutane Da Kamfanoni Ya Haifar Da Da Mai Ido
  • Zaben 2023: Takaddamar Kashi 94 Cikin 100 Na Kujerun Da Aka Lashe Ta Dora Shakku Kan INEC

Gwamna Abba Kabir Yusuf, wanda ya rage kuɗin rajistar shiga jami’a da na zangon karatu da kashi 50 bisa 100 a kwanan baya, ya ƙaddamar da Shirin Bada Tallafin Karatu a Ƙasashen Waje, wanda aka fara ranar Alhamis da jigilar ɗalibai 550 daga Kano.

Gwamna Kabir ya ce, ya ɗora wannan gagarimin aikin alheri ne daga inda tsohon Gwamnan Kano, kuma madugun Kwankwasiyya, Rabi’u Kwankwaso ya tsaya, a lokacin mulkinsa.

Kano

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Ya ce ayyukan alherin da gwamnatin Kwankwaso ta yi wa al’ummar Kano a baya, su na da muhimmancin da ba za a iya daina ci gaba da su ba.

Kabir ya ce, ga shi nan ƙarara ana ta cin moriya da amfanar waɗanda suka je waje karatu a ƙarƙashin gwamnatin Kwankwaso, inda wasu na riƙe da muƙamai sosai a gwamnati da sauran fannonin ayyukan yau da kullum.

Ya lissafa wasu da suka haɗa da Kwamishinan Ilmi Mai Zurfi, Dakta Yusuf Ibrahim, Shugaban Sashen Ƙididdigar Alƙaluma na Jihar Kano, Farfesa Aliyu Isa Aliyu da Mashawarci na Musamman a Fannin Ƙirƙire-ƙirƙire, Dakta Bashir Muzakkir da sauran su.

Gwamnan ya ce, “Bari na bayyana cewa, shi wannan shirin tallafin gurbin karatun waje, madugun mu Sanata Rabi’u Kwankwaso ne ya ƙirƙiro shi.”

Ya ce Kwankwaso sai da ya ɗauki nauyin rukuni-rukunin ɗalibai har rukuni uku zuwa ƙasashe 16 daban-daban.

“Wannan ƙoƙari ya sa an samu nasarar samar da daktoci, masu digiri na biyu da dubban ƙwararrun likitoci, injiniyoyi, matuƙa jirgin sama da gwanayen ayyukan harkokin jiragen ruwa da sauran su.

A jawabin sa tun da farko, Kwankwaso ya gode wa wannan gwamnati ta Abba Kabir, ganin yadda ta ci gaba da ayyukan alherin da ya fara a lokacin ya na Gwamnan Kano.

Kano

Ya ja kunnen ɗaliban su kasance masu ɗa’a kuma jakadun Kano da Nijeriya nagari a duk inda suka samu kan su.

Ɗaliban da dama sun gode wa Gwamnatin Kano, Gwamna Abba da kuma Kwankwaso.

Kafin tashinsu sai da Gwamna Abba Kabir ya damƙa wa kowa kuɗaɗen alawus ɗin sa na daloli a hannu, aka kira su taron dina a Gidan Gwamnati, sannan kuma Gwamna da Kwankwaso suka raka su har cikin jirgi.

Abba da Kwankwaso ba su bar filin jirgin Malam Aminu Kano ba, sai da suka ga tashin jirgin da ya ɗauki ɗaliban.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Kabir YusufkanoKwankwaso
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gidauniyar TY Buratai Ta Nemi ‘Yan Nijeriya Su Kara Hakuri Da Salon Mulkin Tinubu

Next Post

Ina Fatan Fim Ya Yi Sanadiyyar Shiga Ta Gidan Aljanna – Sadiq Sani Sadiq

Related

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

6 hours ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

6 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

8 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

11 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

11 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

12 hours ago
Next Post
Ina Fatan Fim Ya Yi Sanadiyyar Shiga Ta Gidan Aljanna – Sadiq Sani Sadiq

Ina Fatan Fim Ya Yi Sanadiyyar Shiga Ta Gidan Aljanna - Sadiq Sani Sadiq

LABARAI MASU NASABA

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.