ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Tallafa Wa Manoma Mata ‘Yan Kasuwa Na GEEP Ya Kankama A Bauchi

by Sulaiman
3 years ago
Manoma

Sama da manoma da mata ‘yan kasuwa 4,000 ne su ka fara karɓar bashi maras ruwa a ƙarƙashin kashi na biyu na Shirin Haɓaka Kasuwanci, wato ‘Enterprise Empowerment Programme’ ko ‘GEEP 2.0’ na Gwamnatin Tarayya a Jihar Bauchi.

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta ƙaddamar da ba da rancen kwanan nan a garin Bauchi.

  • Ayyukanmu Duk Sun Karade Ko’ina A Fadin Nijeriya —Sadiya Farouq

Masu cin moriyar shirin sun karɓi kuɗaɗe da su ka kama daga naira dubu hamsin (N50,000) har zuwa naira dubu ɗari uku (N300,000), kuma ana sa ran su biya rancen ba tare da wani ruwa da aka ɗora ba a cikin wa’adin shekara ɗaya.

ADVERTISEMENT

A jawabin ta a taron, ministar, wadda kuma ta rarraba agajin tsabar kuɗi ga mutum 5,679, ta yi kira a gare su da su yi amfani da kuɗaɗen wajen yin ƙananan sana’o’i masu riba don inganta rayuwar su.

Ta ce: “Wannan shiri ana aiwatar da shi ne tare da cikakken haɗin gwiwa da gwamnatocin jihohi a matsayin wata kyakkyawar shaida tare da nunin cewa mai girma Shugaban Ƙasa ya sadaukar da kan sa wajen yin aiki kafaɗa da kafaɗa da dukkan matakan gwamnatoci don tunkarar matsalar fatara da yunwa wadda ta zama babban ƙalubalen gina ƙasa da mu ke fuskanta a yau.

LABARAI MASU NASABA

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

“Mun taru a nan ne a yau domin ƙaddamar da shirin Ba Da Lamuni Ga Mutane Mabuƙata (GVG) a Bauchi, Azare da Darazo.

“Shirin na GVG shiri ne na cika alƙawarin Manufofin Buhari ga dukkan mutane mabuƙata, domin a ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen Gwamnatin Shugaba Buhari ga kan talakawa, wanda ya yi daidai da tsarin sa na tausayawa na tsamo ‘yan Nijeriya miliyan 100 daga fatara da yunwa a cikin shekara out.”

An ɗauki ma’aikata ‘yan sa ido kan shirin su 380 waɗanda ake kira ‘Independent Monitors’, kuma an ba su takardun kama aiki nan-take tare da na’urori na musamman da za su yi aikin sa-idon da su domin inganta aikin su.

Bugu da ƙari, an tsara bai wa ‘yan gudun hijira mutum 600 kuɗi N50,000 kowannen su, waɗanda a cikin su akwai naƙasassu da tsofaffi.

Hajiya Sadiya ta ƙara da cewa, “Za a biya kuɗin agaji N50,000 sau ɗaya ga kowane ɗan gudun hijira a ƙarƙashin shirin Agaji da Haɓaka Rayuwar Matasa, wato ‘Youth Empowerment and Social Support Operations’ (YESSO), wanda manufar sa ita ce a inganta ƙwarewar su a ayyukan kasuwanci domin sama wa kai aikin yi, sama wa kai dukiya da kuma sama wa wasu daban aikin yi.

“A Jihar Bauchi, masu cin moriyar shirin mutum 600 ne za a ba agajin tsabar kuɗi N50,000 kowannen su.”

A taron, an ƙaddamar da komfutar biyan kuɗi ta shirin Bayar da Tsabar Kuɗi Bisa Sharuɗɗa, wato ‘Conditional Cash Transfer (CCT) Programme’.

A cewar mai tallafa wa ministar a fagen aikin jarida, Miss Nneka Ikem Anibeze, muhimmancin wannan shiri shi ne a samar da matattarar bayanai mai inganci, ta gaskiya, kuma mai sauƙin sarrafawa domin biyan kuɗaɗe ga masu cin moriyar shirin na Bayar da Kuɗi Bisa Sharuɗɗa, wato ‘Conditional Cash Transfer (CCT) Programme’.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso
Labarai

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Next Post
Ba Mu Tauye Wa Kowa Damar Mallakar Katin Zabe A Kasar Nan Ba – INEC

Ba Mu Tauye Wa Kowa Damar Mallakar Katin Zabe A Kasar Nan Ba - INEC

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.