ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Tallafa Wa Manoma Mata ‘Yan Kasuwa Na GEEP Ya Kankama A Bauchi

by Sulaiman
4 years ago
Manoma

Sama da manoma da mata ‘yan kasuwa 4,000 ne su ka fara karɓar bashi maras ruwa a ƙarƙashin kashi na biyu na Shirin Haɓaka Kasuwanci, wato ‘Enterprise Empowerment Programme’ ko ‘GEEP 2.0’ na Gwamnatin Tarayya a Jihar Bauchi.

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta ƙaddamar da ba da rancen kwanan nan a garin Bauchi.

  • Ayyukanmu Duk Sun Karade Ko’ina A Fadin Nijeriya —Sadiya Farouq

Masu cin moriyar shirin sun karɓi kuɗaɗe da su ka kama daga naira dubu hamsin (N50,000) har zuwa naira dubu ɗari uku (N300,000), kuma ana sa ran su biya rancen ba tare da wani ruwa da aka ɗora ba a cikin wa’adin shekara ɗaya.

ADVERTISEMENT

A jawabin ta a taron, ministar, wadda kuma ta rarraba agajin tsabar kuɗi ga mutum 5,679, ta yi kira a gare su da su yi amfani da kuɗaɗen wajen yin ƙananan sana’o’i masu riba don inganta rayuwar su.

Ta ce: “Wannan shiri ana aiwatar da shi ne tare da cikakken haɗin gwiwa da gwamnatocin jihohi a matsayin wata kyakkyawar shaida tare da nunin cewa mai girma Shugaban Ƙasa ya sadaukar da kan sa wajen yin aiki kafaɗa da kafaɗa da dukkan matakan gwamnatoci don tunkarar matsalar fatara da yunwa wadda ta zama babban ƙalubalen gina ƙasa da mu ke fuskanta a yau.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

“Mun taru a nan ne a yau domin ƙaddamar da shirin Ba Da Lamuni Ga Mutane Mabuƙata (GVG) a Bauchi, Azare da Darazo.

“Shirin na GVG shiri ne na cika alƙawarin Manufofin Buhari ga dukkan mutane mabuƙata, domin a ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen Gwamnatin Shugaba Buhari ga kan talakawa, wanda ya yi daidai da tsarin sa na tausayawa na tsamo ‘yan Nijeriya miliyan 100 daga fatara da yunwa a cikin shekara out.”

An ɗauki ma’aikata ‘yan sa ido kan shirin su 380 waɗanda ake kira ‘Independent Monitors’, kuma an ba su takardun kama aiki nan-take tare da na’urori na musamman da za su yi aikin sa-idon da su domin inganta aikin su.

Bugu da ƙari, an tsara bai wa ‘yan gudun hijira mutum 600 kuɗi N50,000 kowannen su, waɗanda a cikin su akwai naƙasassu da tsofaffi.

Hajiya Sadiya ta ƙara da cewa, “Za a biya kuɗin agaji N50,000 sau ɗaya ga kowane ɗan gudun hijira a ƙarƙashin shirin Agaji da Haɓaka Rayuwar Matasa, wato ‘Youth Empowerment and Social Support Operations’ (YESSO), wanda manufar sa ita ce a inganta ƙwarewar su a ayyukan kasuwanci domin sama wa kai aikin yi, sama wa kai dukiya da kuma sama wa wasu daban aikin yi.

“A Jihar Bauchi, masu cin moriyar shirin mutum 600 ne za a ba agajin tsabar kuɗi N50,000 kowannen su.”

A taron, an ƙaddamar da komfutar biyan kuɗi ta shirin Bayar da Tsabar Kuɗi Bisa Sharuɗɗa, wato ‘Conditional Cash Transfer (CCT) Programme’.

A cewar mai tallafa wa ministar a fagen aikin jarida, Miss Nneka Ikem Anibeze, muhimmancin wannan shiri shi ne a samar da matattarar bayanai mai inganci, ta gaskiya, kuma mai sauƙin sarrafawa domin biyan kuɗaɗe ga masu cin moriyar shirin na Bayar da Kuɗi Bisa Sharuɗɗa, wato ‘Conditional Cash Transfer (CCT) Programme’.

Manoma
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya
  • Sulaiman
    Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari
  • Sulaiman
    Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya
  • Sulaiman
    Hadin Gwiwar BRICS Na Jagorantar Hadin Kan Kasashe Masu Tasowa Da Dogaro Da Karfin Kansu

MASU ALAKA

Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi
Manyan Labarai

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

September 15, 2026
Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa
Manyan Labarai

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

September 15, 2026
Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba
Manyan Labarai

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

September 15, 2026
Next Post
Ba Mu Tauye Wa Kowa Damar Mallakar Katin Zabe A Kasar Nan Ba – INEC

Ba Mu Tauye Wa Kowa Damar Mallakar Katin Zabe A Kasar Nan Ba - INEC

LABARAI MASU NASABA

Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

September 15, 2026
Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

September 15, 2026
Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

September 15, 2026
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Arziƙin Dangote Ya Haura Dala Biliyan 50 Bayan Fara Sayar Da Hannun Jarin Matatarsa – Forbes

September 15, 2026
Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

September 14, 2026
Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

Duk Wani Yunkuri Na Karfafa Burin Japan Na Fadada Karfin Soji Zai Jefa Yankin Cikin Hadari

September 14, 2026
Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

Tsohon Firaminsitan Jordan: Kasar Sin Tana Kan Gaba Wajen Gudanar Da Fasahar AI A Duniya

September 14, 2026
Hadin Gwiwar BRICS Na Jagorantar Hadin Kan Kasashe Masu Tasowa Da Dogaro Da Karfin Kansu

Hadin Gwiwar BRICS Na Jagorantar Hadin Kan Kasashe Masu Tasowa Da Dogaro Da Karfin Kansu

September 14, 2026
Na Miƙa Kaina Ga Hukumomin Tsaro – Sanata Shehu Buba

Na Miƙa Kaina Ga Hukumomin Tsaro – Sanata Shehu Buba

September 14, 2026
Sin Na Shirin Fadada Samar Da Hidimomin Reno Da Na Kiwon Lafiyar Yara Masu Rahusa

Sin Na Shirin Fadada Samar Da Hidimomin Reno Da Na Kiwon Lafiyar Yara Masu Rahusa

September 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.