ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Tallafa Wa Manoma Mata ‘Yan Kasuwa Na GEEP Ya Kankama A Bauchi

by Sulaiman
4 years ago
Manoma

Sama da manoma da mata ‘yan kasuwa 4,000 ne su ka fara karɓar bashi maras ruwa a ƙarƙashin kashi na biyu na Shirin Haɓaka Kasuwanci, wato ‘Enterprise Empowerment Programme’ ko ‘GEEP 2.0’ na Gwamnatin Tarayya a Jihar Bauchi.

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta ƙaddamar da ba da rancen kwanan nan a garin Bauchi.

  • Ayyukanmu Duk Sun Karade Ko’ina A Fadin Nijeriya —Sadiya Farouq

Masu cin moriyar shirin sun karɓi kuɗaɗe da su ka kama daga naira dubu hamsin (N50,000) har zuwa naira dubu ɗari uku (N300,000), kuma ana sa ran su biya rancen ba tare da wani ruwa da aka ɗora ba a cikin wa’adin shekara ɗaya.

ADVERTISEMENT

A jawabin ta a taron, ministar, wadda kuma ta rarraba agajin tsabar kuɗi ga mutum 5,679, ta yi kira a gare su da su yi amfani da kuɗaɗen wajen yin ƙananan sana’o’i masu riba don inganta rayuwar su.

Ta ce: “Wannan shiri ana aiwatar da shi ne tare da cikakken haɗin gwiwa da gwamnatocin jihohi a matsayin wata kyakkyawar shaida tare da nunin cewa mai girma Shugaban Ƙasa ya sadaukar da kan sa wajen yin aiki kafaɗa da kafaɗa da dukkan matakan gwamnatoci don tunkarar matsalar fatara da yunwa wadda ta zama babban ƙalubalen gina ƙasa da mu ke fuskanta a yau.

LABARAI MASU NASABA

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

“Mun taru a nan ne a yau domin ƙaddamar da shirin Ba Da Lamuni Ga Mutane Mabuƙata (GVG) a Bauchi, Azare da Darazo.

“Shirin na GVG shiri ne na cika alƙawarin Manufofin Buhari ga dukkan mutane mabuƙata, domin a ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen Gwamnatin Shugaba Buhari ga kan talakawa, wanda ya yi daidai da tsarin sa na tausayawa na tsamo ‘yan Nijeriya miliyan 100 daga fatara da yunwa a cikin shekara out.”

An ɗauki ma’aikata ‘yan sa ido kan shirin su 380 waɗanda ake kira ‘Independent Monitors’, kuma an ba su takardun kama aiki nan-take tare da na’urori na musamman da za su yi aikin sa-idon da su domin inganta aikin su.

Bugu da ƙari, an tsara bai wa ‘yan gudun hijira mutum 600 kuɗi N50,000 kowannen su, waɗanda a cikin su akwai naƙasassu da tsofaffi.

Hajiya Sadiya ta ƙara da cewa, “Za a biya kuɗin agaji N50,000 sau ɗaya ga kowane ɗan gudun hijira a ƙarƙashin shirin Agaji da Haɓaka Rayuwar Matasa, wato ‘Youth Empowerment and Social Support Operations’ (YESSO), wanda manufar sa ita ce a inganta ƙwarewar su a ayyukan kasuwanci domin sama wa kai aikin yi, sama wa kai dukiya da kuma sama wa wasu daban aikin yi.

“A Jihar Bauchi, masu cin moriyar shirin mutum 600 ne za a ba agajin tsabar kuɗi N50,000 kowannen su.”

A taron, an ƙaddamar da komfutar biyan kuɗi ta shirin Bayar da Tsabar Kuɗi Bisa Sharuɗɗa, wato ‘Conditional Cash Transfer (CCT) Programme’.

A cewar mai tallafa wa ministar a fagen aikin jarida, Miss Nneka Ikem Anibeze, muhimmancin wannan shiri shi ne a samar da matattarar bayanai mai inganci, ta gaskiya, kuma mai sauƙin sarrafawa domin biyan kuɗaɗe ga masu cin moriyar shirin na Bayar da Kuɗi Bisa Sharuɗɗa, wato ‘Conditional Cash Transfer (CCT) Programme’.

Manoma
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17
  • Sulaiman
    Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

MASU ALAKA

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato
Manyan Labarai

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027
Manyan Labarai

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000
Labarai

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Next Post
Ba Mu Tauye Wa Kowa Damar Mallakar Katin Zabe A Kasar Nan Ba – INEC

Ba Mu Tauye Wa Kowa Damar Mallakar Katin Zabe A Kasar Nan Ba - INEC

LABARAI MASU NASABA

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

Sin Tana Matsayi Na Farko A Duniya A Fannin Kirkire-kirkiren Wutar Lantarki

July 12, 2026
Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

Mahara Sun Kashe Mutane 9 Ƴan Gida Ɗaya, Har Da Jariri Ɗan Wata 2 A Filato

July 12, 2026
Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

Sin Ta Yi Kunnen Doki Da Nijeriya A Gasar Kwallon Kafa Tsakanin Kasashe 4 Ta ‘Yan Kasa Da 17

July 12, 2026
FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Fitar Da Sanarwa Game Da Cika Shekaru 10 Da Fitar Da Hukuncin Takkadamar “Philippines Da China”

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jadadda Bukatar Kare Rayuka Da Dukiyoyin Jama’a Yayin Rangadi A Beijing

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.