• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin X Space Na LEADERSHIP: Tabbas Gwamnatin Kano Ta Hau Turbar Bunkasa Ilimi – Mahalarta

by Naziru Adam Ibrahim
1 year ago
Kano

Masu ruwa da tsaki a fannin ilimi sun yaba wa kokarin Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, wajen inganta bangaren duba da gagarumar nasarar da ake samu biyo bayan ayyana dokar ta baci da ya yi a fannin ilimin jihar.

Sun bayyana hakan ne cikin shirin tattaunawa da LEADERSHIP ta shirya a shafinta na X da akafi sani da twitter inda masu ruwa da tsakin suka yaba da da matakan da gwamnatin ke dauka.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Matafiya A Babbar Hanyar Gusau-Funtua
  • Xi Jinping Ya Yi Rangadi A Birnin Baoji Na Lardin Shaanxi Da Birnin Tianshui Na Lardin Gansu

Cikin jawabinta, babbar hadimar Gwamna Abba Kabir Yusuf, kan ilimin Mata  Hajiya Yesmin Mukhtar, ta ce gwamnan ya gyara makarantu da dama da ke cikin halin kaka-ni-ka-yi tare da bude wasu da a da can baya an nuna musu halin ko in kula.

Sauran ci gaban da aka samu kamar yadda sauran masu tofa albarkacin bakinsu irin su tsohon Kwamishinan Ilimi na Jihar Kaduna, Farfesa Usman Moddibo da mai mallakar shafin Arewa Twitter, Malam Abdullahi Nasarawa suka bayyana, akwai kaddamar da manyan ayyuka na gyaran makarantu da kuma inganta kwazazon malamai.

Duk sun yaba wa gwamnatin jihar kan wasu daga cikin jiga-jigan kokarinta na inganta harkar ilimin irin su ware kaso 29 na kasafin jihar ga bangaren ilimi da diban malamai fiye da 5,600 da biyan kudaden jarrabawar WAEC da NECO ga dalibai da bude cibiyoyin samun ilimin zamani na na’ura mai kwakwalwa.

LABARAI MASU NASABA

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Sai dai sun ce duk da haka akwai sauran aiki a gaba wanda idan aka mayar da hankali tabbas za a yi nasarar har karshe.

Shi ma kwamishinan ilimi na Jihar Kano, Alhaji Umar Haruna Doguwa ya bayyana bukatar yaba kokarin da gwamnatin ke yi ta hanyar ba ta duk wani hadin kai da take bukata don samun nasara.

Zuwa yanzu dai, daga cikin gagarumin kokarin da take yi, Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta fitar da fiye da Naira Biliyan 2.7 domin gina ajujuwa 176 da ofisoshi 88 a sassan kananan hukumomin jihar 44.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

gombe
Ilimi

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma
Ilimi

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
ASUU
Ilimi

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Next Post
Ƴan Bindiga Sun Tare Hanyar Zamfara, Sun Sace Matafiya 150

Ƴan Bindiga Sun Tare Hanyar Zamfara, Sun Sace Matafiya 150

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

Kasar Sin Ta Tsara Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Na 15

October 25, 2025
Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025 Justine Madugu

October 25, 2025
An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

An Kaddamar Da Nuna Muhimman Shirye-shiryen CMG A Membobin APEC

October 25, 2025
Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

Zuwan Tsoffin ’Yan Wasan Barcelona Abuja Ya Nuna Ana Samun Zaman Lafiya A Nijeriya – Matawalle

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025 Dakta Seidu Adebayo Bello

October 25, 2025
Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kuɗaɗe Na Shekarar 2025, Opay Nigeria

October 25, 2025

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025, Kamfanin Nestlé Pure Life

October 25, 2025
Mata Ne Ginshikin Ci-Gaban Al’umma – Gimbiyar Dange

Mata Ne Ginshikin Ci-Gaban Al’umma – Gimbiyar Dange

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.