• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Zamanantar Da Aikin Noma Na Sin Na Samar Da Damar Bunkasa Bangaren A Afirka 

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Noma

Kwanan baya, kasar Sin ta gabatar da takardar farko ta bana, wadda ta kasance a matsayin sanarwar farko ta manufofin gwamnati da mahukuntan tsakiya na kasar Sin suke fitarwa a farkon kowace shekara, wadda ake daukarta a matsayin manunin muhimman manufofin da gwamnati za ta fi bai wa fifiko. Inda a karo na farko, takardar ta gabatar da manufar “raya sabon ginshikin bunkasa ayyukan gona”, da zummar tattara abubuwa na zamani dake shafar samar da kayayyaki. Alkaluman da hukumar aikin noma da raya karkara ta Sin ta samar sun shaida cewa, yawan gudunmawar da ci gaban kimiyya da fasaha a bangaren aikin noma ta bayar ya kai kashi 63.2% a shekarar 2024.

Alal hakika, bunkasar aikin noma a bangaren kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha ya fidda wata sabuwar hanya ta hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin zamanantar da aikin gona. A halin yanzu, shinkafa da ake tagwaitawa mai fasahar Sin ta samu karbuwa a kasashen Afirka fiye da 20, matakin da ya taimakawa wadannan kasashe wajen daga yawan shinkafa da suke samu daga ton 2 a ko wace hekta zuwa 7.5. Ya zuwa karshen shekarar 2023, Sin ta kafa cibiyoyin ba da misali kan kimiyyar aikin noma 24 a kasashen Afirka, inda ake kokarin yayata fasahar shuka masara mai matukar armashi da fasahar shuka kayayyakin lambu da hayayyafar rogo mai saurin nuna da dai sauran fasahohi na zamani fiye da 300, kana manoma fiye da miliyan 1 suna cin gajiyarsu, wadanda suka yi matukar tallafa wa aikin zamanantar da aikin gona a nahiyar.

Hadin gwiwar Sin da Afirka a bangaren zamanantar da aikin gona hakikanin mataki ne da Sin ta dauka na gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga dukkan al’umma a bangaren aikin noma, wanda ya taimakawa kasashen Afirka wajen samun isasshen hatsi na dogaro da kansu ta amfani da karfin kirkire-kirkire a bangaren aikin gona. Kuma ta zama abin koyi na kulla sabon salon huldar kasa da kasa na hadin gwiwar cin moriyar juna da samun bunkasa tare. (Mai zane da rubutu : MINA)

 

 

LABARAI MASU NASABA

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Ra'ayi Riga

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani
Ra'ayi Riga

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Next Post
Jama’ar Duniya Sun Soki Matakin Amurka Na Matsawa Kasashe Ta Hanyar Kakaba Haraji 

Jama’ar Duniya Sun Soki Matakin Amurka Na Matsawa Kasashe Ta Hanyar Kakaba Haraji 

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.