• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirye-shiryen Saukar Buhari Mulki…

by Bello Hamza and El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Shirye-shiryen Saukar Buhari Mulki…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da ‘yan Nijeriya ke tsumayar zuwan ranar 29 ga watan Mayu, ranar da za a rantsar da zababben Shugaban Kasa, Bola Tinubu, tuni shirye-shirye suka yi nisa na saukar mulkin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari tare da mika ragama ga sabuwar gwamnati.

Daga abubuwan da ke gudana a Abuja na shirin saukar Shugaba Buhari, akwai batun sauyin muhalli. Dama an saba, duk lokacin da za a yi canjin gwamnati, manyan muhimman ‘yan siyasan kasar nan musamman wadanda ke zaune a gidajen gwamnati kan tattara nau-i-nasu zuwa inda za su ci gaba da rayuwa bayan sauka daga karagar mulki.

  • Shugaban Tsimi Da Tanadi Ya Warware Mishkilar Dimbin Bashin Da Ake Bin Jihar Kaduna
  • Masana: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Za Ta Sa A Samu Sabuwar Damar Zamanintar Da Nahiyar Afirka

Daya daga cikin tsare-tsaren da aka yi a fadar shugaban kasa ta ‘Aso Rocka’ shi ne sauyin muhallin shugaban kasa da iyalinsa daga babban gidan shugaban kasa na fadar zuwa wani gid ana musamman da ake ce wa ‘Gidan Gilashi’, watau ‘Glass House’. Wani gida ne da aka kebe wa shugaban kasa mai barin gado inda zai koma ya zauna na kwanakin karshe na barin mulkinsa har zuwa ranar da za a rantsar da sabon shugaban kasa.

Idan za a iya tunawa, uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari a lokacin da take zagayawa da uwargidan zabbaben shugaban kasa mai jiran gado a makon da ya gabata, ta bayyana cewa tuni ita da maigidanta shugaba Buhari suka koma Gidan Gilashi inda za su zauna har ranar da za a kaddamar da sabuwar gwamnati, daga nan kuma su zarce Daura ta Jihar Katsina, mahaifar Shugaba Buhari.

Haka kuma, bisa al’adar shirin karbar ragama, bayan tabbatar da nasarar sabon shugaban da za a mika wa ragamar mulki, zabbaben shugaban kasa kan koma wani gidan da aka yi wa lakabi da ‘Gidan Tsaro’, watau ‘Defense House’ da ke unguwar Maitama Abuja, inda a nan zai zauna ya rika shirye-shiryen bikin rantsar da shi.

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Tsarin da aka yi na komawar shugaban kasa mai barin gado zuwa gidan gilashi daga asalin gidan shugaban kasa na fadar gwamnati, wani shiri ne da sojoji ke kira “Tactical withdrawal” watau janyewa a sannu a hankali.

Zama a wannan gidan yana da hikimomi kamar guda biyu, zai samar wa da shugaba mai barin gado wajen zama a yayin da ake sake yi wa gidan shugaban kasa kwaskwarima don ya yi daidai da yadda zababben shugaban kasa da mutanesa ke so.

Shugaba mai barin gado zai ci gaba da zama a gidan gilashi har zuwa lokacin da zai kammala wa’adin mulkinsa.

Babban aikin gidan gilashi shi ne, ya kasance wurin da shugaban kasa mai barin gado zai zauna ya kammala tsare-tsaren mika mulki tsakaninsa da gwamnati mai kamawa. Bayan an kadamar da sabuwar gamnati, ba za a sake amfani da gidan ba sai zuwa lokacin da aka samu sabon shugaba da za a mika wa gama.

Wannan wata al’ada ce ta dora Nijeriya a turbar mika mulki ga gwamnati mai shigowa ckin kwanciyar hankali.

A wasu bangare kuma ana ci gaba da tarurruka na a tsakanin wakilan gwamnati mai barin gado da gwamnati mai kamawa domin ganin shirye-shiryen mika ragamar mulkin sun kankama ba tare da kama hannun yaro ba. Har ila yau, duk dai a Abujar, an shirya horaswa ga sabbin ‘yan majalisa da sabbin gwamnoni da gwamnonin masu barin gado kan hanyoyin da za a yi aiki tare domin samun nasarar mika ragamar mulki da kuma yadda sabbon shugabannin da aka zaba za su fara da kafar dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Buhari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaban Tsimi Da Tanadi Ya Warware Mishkilar Dimbin Bashin Da Ake Bin Jihar Kaduna

Next Post

Shimfida: Aikin Hajji Da Batun Tsallaka Mikati Ba Tare Da Harama Ba

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

27 minutes ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

2 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

3 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

5 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

8 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

8 hours ago
Next Post
Shimfida: Aikin Hajji Da Batun Tsallaka Mikati Ba Tare Da Harama Ba

Shimfida: Aikin Hajji Da Batun Tsallaka Mikati Ba Tare Da Harama Ba

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.