ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirye-shiryen Saukar Buhari Mulki…

by Bello Hamza and El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Buhari

A yayin da ‘yan Nijeriya ke tsumayar zuwan ranar 29 ga watan Mayu, ranar da za a rantsar da zababben Shugaban Kasa, Bola Tinubu, tuni shirye-shirye suka yi nisa na saukar mulkin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari tare da mika ragama ga sabuwar gwamnati.

Daga abubuwan da ke gudana a Abuja na shirin saukar Shugaba Buhari, akwai batun sauyin muhalli. Dama an saba, duk lokacin da za a yi canjin gwamnati, manyan muhimman ‘yan siyasan kasar nan musamman wadanda ke zaune a gidajen gwamnati kan tattara nau-i-nasu zuwa inda za su ci gaba da rayuwa bayan sauka daga karagar mulki.

  • Shugaban Tsimi Da Tanadi Ya Warware Mishkilar Dimbin Bashin Da Ake Bin Jihar Kaduna
  • Masana: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Za Ta Sa A Samu Sabuwar Damar Zamanintar Da Nahiyar Afirka

Daya daga cikin tsare-tsaren da aka yi a fadar shugaban kasa ta ‘Aso Rocka’ shi ne sauyin muhallin shugaban kasa da iyalinsa daga babban gidan shugaban kasa na fadar zuwa wani gid ana musamman da ake ce wa ‘Gidan Gilashi’, watau ‘Glass House’. Wani gida ne da aka kebe wa shugaban kasa mai barin gado inda zai koma ya zauna na kwanakin karshe na barin mulkinsa har zuwa ranar da za a rantsar da sabon shugaban kasa.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa, uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari a lokacin da take zagayawa da uwargidan zabbaben shugaban kasa mai jiran gado a makon da ya gabata, ta bayyana cewa tuni ita da maigidanta shugaba Buhari suka koma Gidan Gilashi inda za su zauna har ranar da za a kaddamar da sabuwar gwamnati, daga nan kuma su zarce Daura ta Jihar Katsina, mahaifar Shugaba Buhari.

Haka kuma, bisa al’adar shirin karbar ragama, bayan tabbatar da nasarar sabon shugaban da za a mika wa ragamar mulki, zabbaben shugaban kasa kan koma wani gidan da aka yi wa lakabi da ‘Gidan Tsaro’, watau ‘Defense House’ da ke unguwar Maitama Abuja, inda a nan zai zauna ya rika shirye-shiryen bikin rantsar da shi.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Tsarin da aka yi na komawar shugaban kasa mai barin gado zuwa gidan gilashi daga asalin gidan shugaban kasa na fadar gwamnati, wani shiri ne da sojoji ke kira “Tactical withdrawal” watau janyewa a sannu a hankali.

Zama a wannan gidan yana da hikimomi kamar guda biyu, zai samar wa da shugaba mai barin gado wajen zama a yayin da ake sake yi wa gidan shugaban kasa kwaskwarima don ya yi daidai da yadda zababben shugaban kasa da mutanesa ke so.

Shugaba mai barin gado zai ci gaba da zama a gidan gilashi har zuwa lokacin da zai kammala wa’adin mulkinsa.

Babban aikin gidan gilashi shi ne, ya kasance wurin da shugaban kasa mai barin gado zai zauna ya kammala tsare-tsaren mika mulki tsakaninsa da gwamnati mai kamawa. Bayan an kadamar da sabuwar gamnati, ba za a sake amfani da gidan ba sai zuwa lokacin da aka samu sabon shugaba da za a mika wa gama.

Wannan wata al’ada ce ta dora Nijeriya a turbar mika mulki ga gwamnati mai shigowa ckin kwanciyar hankali.

A wasu bangare kuma ana ci gaba da tarurruka na a tsakanin wakilan gwamnati mai barin gado da gwamnati mai kamawa domin ganin shirye-shiryen mika ragamar mulkin sun kankama ba tare da kama hannun yaro ba. Har ila yau, duk dai a Abujar, an shirya horaswa ga sabbin ‘yan majalisa da sabbin gwamnoni da gwamnonin masu barin gado kan hanyoyin da za a yi aiki tare domin samun nasarar mika ragamar mulki da kuma yadda sabbon shugabannin da aka zaba za su fara da kafar dama.

Buhari
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ƙungiyar Kansilolin APC Ta Yi Barazanar Janye Goyon Bayanta Idan Ba A Daina Zargin Sanata Yari Ba
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya
Buhari
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Next Post
Shimfida: Aikin Hajji Da Batun Tsallaka Mikati Ba Tare Da Harama Ba

Shimfida: Aikin Hajji Da Batun Tsallaka Mikati Ba Tare Da Harama Ba

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.