ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirye-shiryen Saukar Buhari Mulki…

by Bello Hamza and El-Zaharadeen Umar
3 years ago
Buhari

A yayin da ‘yan Nijeriya ke tsumayar zuwan ranar 29 ga watan Mayu, ranar da za a rantsar da zababben Shugaban Kasa, Bola Tinubu, tuni shirye-shirye suka yi nisa na saukar mulkin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari tare da mika ragama ga sabuwar gwamnati.

Daga abubuwan da ke gudana a Abuja na shirin saukar Shugaba Buhari, akwai batun sauyin muhalli. Dama an saba, duk lokacin da za a yi canjin gwamnati, manyan muhimman ‘yan siyasan kasar nan musamman wadanda ke zaune a gidajen gwamnati kan tattara nau-i-nasu zuwa inda za su ci gaba da rayuwa bayan sauka daga karagar mulki.

  • Shugaban Tsimi Da Tanadi Ya Warware Mishkilar Dimbin Bashin Da Ake Bin Jihar Kaduna
  • Masana: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Za Ta Sa A Samu Sabuwar Damar Zamanintar Da Nahiyar Afirka

Daya daga cikin tsare-tsaren da aka yi a fadar shugaban kasa ta ‘Aso Rocka’ shi ne sauyin muhallin shugaban kasa da iyalinsa daga babban gidan shugaban kasa na fadar zuwa wani gid ana musamman da ake ce wa ‘Gidan Gilashi’, watau ‘Glass House’. Wani gida ne da aka kebe wa shugaban kasa mai barin gado inda zai koma ya zauna na kwanakin karshe na barin mulkinsa har zuwa ranar da za a rantsar da sabon shugaban kasa.

ADVERTISEMENT

Idan za a iya tunawa, uwargidan shugaban kasa, Aisha Buhari a lokacin da take zagayawa da uwargidan zabbaben shugaban kasa mai jiran gado a makon da ya gabata, ta bayyana cewa tuni ita da maigidanta shugaba Buhari suka koma Gidan Gilashi inda za su zauna har ranar da za a kaddamar da sabuwar gwamnati, daga nan kuma su zarce Daura ta Jihar Katsina, mahaifar Shugaba Buhari.

Haka kuma, bisa al’adar shirin karbar ragama, bayan tabbatar da nasarar sabon shugaban da za a mika wa ragamar mulki, zabbaben shugaban kasa kan koma wani gidan da aka yi wa lakabi da ‘Gidan Tsaro’, watau ‘Defense House’ da ke unguwar Maitama Abuja, inda a nan zai zauna ya rika shirye-shiryen bikin rantsar da shi.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Tsarin da aka yi na komawar shugaban kasa mai barin gado zuwa gidan gilashi daga asalin gidan shugaban kasa na fadar gwamnati, wani shiri ne da sojoji ke kira “Tactical withdrawal” watau janyewa a sannu a hankali.

Zama a wannan gidan yana da hikimomi kamar guda biyu, zai samar wa da shugaba mai barin gado wajen zama a yayin da ake sake yi wa gidan shugaban kasa kwaskwarima don ya yi daidai da yadda zababben shugaban kasa da mutanesa ke so.

Shugaba mai barin gado zai ci gaba da zama a gidan gilashi har zuwa lokacin da zai kammala wa’adin mulkinsa.

Babban aikin gidan gilashi shi ne, ya kasance wurin da shugaban kasa mai barin gado zai zauna ya kammala tsare-tsaren mika mulki tsakaninsa da gwamnati mai kamawa. Bayan an kadamar da sabuwar gamnati, ba za a sake amfani da gidan ba sai zuwa lokacin da aka samu sabon shugaba da za a mika wa gama.

Wannan wata al’ada ce ta dora Nijeriya a turbar mika mulki ga gwamnati mai shigowa ckin kwanciyar hankali.

A wasu bangare kuma ana ci gaba da tarurruka na a tsakanin wakilan gwamnati mai barin gado da gwamnati mai kamawa domin ganin shirye-shiryen mika ragamar mulkin sun kankama ba tare da kama hannun yaro ba. Har ila yau, duk dai a Abujar, an shirya horaswa ga sabbin ‘yan majalisa da sabbin gwamnoni da gwamnonin masu barin gado kan hanyoyin da za a yi aiki tare domin samun nasarar mika ragamar mulki da kuma yadda sabbon shugabannin da aka zaba za su fara da kafar dama.

Buhari
Bello Hamza
+ posts Bio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina
Buhari
El-Zaharadeen Umar
+ posts Bio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Shimfida: Aikin Hajji Da Batun Tsallaka Mikati Ba Tare Da Harama Ba

Shimfida: Aikin Hajji Da Batun Tsallaka Mikati Ba Tare Da Harama Ba

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.