• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Xi Jinping Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Afirka Ta Kudu Da Na Kasar Senegal

by CMG Hausa
3 years ago
Senegal

Da yammacin yau Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa a tsibirin Bali dake kasar Indonesia.

A yayin ganawar, shugaba Xi Jinping ya yi nuni da cewa, Sin tana raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Afirka ta Kudu bisa manyan tsare-tsare, kuma tana son su kara imani da juna a fannin siyasa, da sa kaimi ga samun ci gaba kan raya dangantakarsu a dukkan fannoni.

  • Xi Jinping: Sin Na Goyon Bayan Shigar Da Kungiyar AU G20

Ya ce Sin tana son yin mu’amala da kasar Afirka ta Kudu kan fasahohin tafiyar da harkokin siyasa da kasa, da goyon bayan Afirka ta Kudu wajen neman hanyar zamanintar da kanta bisa nata salo, da kara hadin gwiwa tsakanin shawarar “ziri daya da hanya daya” da shirin sake bunkasa tattalin arziki da farfadowa na kasar Afirka ta Kudu, da zurfafa hadin gwiwarsu a fannonin cinikayya da zuba jari, da makamashi da sauransu, da sa kaimi ga aiwatar da ayyukan da aka cimma daidaito kansu a gun taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, wanda aka yi a kasar ta Afirka ta Kudu, da goyon bayan kamfanonin Sin don su zuba jari a kasar, da kuma fadada fitar da kayayyakin Afirka ta Kudu zuwa kasar Sin.

A nasa bangare, shugaba Ramaphosa ya bayyana cewa, Sin muhimmiyar abokiya ce ta kasar Afirka ta Kudu bisa manyan tsare-tsare, kuma kasarsa za ta ci gaba da goyon bayan ka’idar Sin daya tak a duniya. Kana Afirka ta Kudu tana son koyon fasahohin Sin a fannonin samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba, da kyautata tsarin makamashi, da shiga ayyukan raya shawarar “ziri daya da hanya daya”, da kuma kara bude kofa ga kamfanonin Sin don sa kaimi gare su, wajen zuba jari da hadin gwiwa a kasar.

Yau da yamma, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na kasar Senegal Macky Sall a tsibirin Bali dake kasar Indonesia.

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Shugaba Xi Jinping ya yi nuni da cewa, bisa kokarin bangarorin biyu, an samu babban ci gaba kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da Senegal da kuma Afirka.

Ya ce Sin tana son ci gaba da yin kokari tare da kasar Senegal wajen samun bunkasuwa da farfadowa, da goyon bayan juna kan batutuwan dake shafar cikakken ‘yancinsu, da tsaron kasa, da moriyar bunkasuwa. Ya kara da cewa, Sin tana son ci gaba da nuna goyon baya ga kasar Senegal wajen gina ayyukan more rayuwa kamar hanyoyin mota, da yankin masana’antu, da kuma fadada fitar da kayayyakin amfanin gona zuwa kasar Sin.

A nasa bangare, shugaba Sall ya godewa kasar Sin bisa gudummawarta ga Senegal da kuma sauran kasashen Afirka, yana mai cewa ta kasance kasa ta farko da ta goyi bayan shigar da kungiyar AU cikin kungiyar G20.

Ya ce kasar Senegal ta gamsu da ci gaban da aka samu kan ayyukan da aka cimma daidaito kansu, a gun taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Afirka, kana tana son ci gaba da hada gwiwa bisa tsarin dandalin tattaunawar.

A wannan rana kuma, shugaba Xi ya gana da firaministan kasar Netherland Mark Rutte, da firaministan kasar Australia Anthony Albanese, da shugaban kasar Argentina Alberto Fernández, da firaministan kasar Spaniya Pedro Sánchez, da kuma shugaban kasar Koriya ta Kudu Yoon Seok-Youl. (Zainab)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai
Daga Birnin Sin

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik
Daga Birnin Sin

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Next Post
Dan Majalisar Dokokin Jihar Legas, Abdulsobur Omititi Ya Rasu A Wajen Taron Tinubu A Jos 

Dan Majalisar Dokokin Jihar Legas, Abdulsobur Omititi Ya Rasu A Wajen Taron Tinubu A Jos 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Senegal

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Sauya Sunayen Waɗanda Aka Yi Wa Afuwa

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.