• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Amurka

by CMG Hausa
2 years ago
in Labarai
0
Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden, sun gudanar da taron koli a rukunin gidajen alfarma na Filoli, dake birnin San Francisco na kasar Amurka jiya Laraba agogon wurin, inda suka yi musayar ra’ayoyi da ma bayanai kan muhimman batutuwa masu sarkakiya dake da muhimmanci ga alkiblar dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, da manyan batutuwan da suka shafi zaman lafiya da ci gaban duniya.

Shugaba Xi Jinping ya bayyana cewa, ga kasashen Sin da Amurka, juya wa juna baya ba shi ne zabi ba. Ba gaskiya ba ne wani bangare ya sakewa wani bangare fasali. Kuma rikici da nuna adawa na iya haifar da sakamakon da bangarorin biyu ba za su iya jurewa ba.

Haka kuma takarar manyan kasashe, ba za ta iya magance matsalolin da ke addabar Sin da Amurka ko duniya ba. Duniya tana da girman da ƙasashen biyu za su sakata su wala, kuma nasarar wata kasa dama ce ga wata.

  • Shugaba Xi Ya Isa Birnin San Francisco Don Ganawa Da Takwaransa Na Amurka Da Halartar Taron Shugabannin Mambobin Kungiyar APEC

 

Shugaban na kasar Sin ya kuma yi karin haske, kan muhimman sigogin tsarin zamanintar da kasar Sin da ma’anarsa, da ci gaban da kasar Sin ke samu, da kuma manufarta bisa manyan tsare-tsare. Ya yi nuni da cewa, kasar Sin tana kokarin farfado da al’ummar Sinawa daga dukkan fannoni ta hanyar zamanantar da kasar. Don haka, ba za ta koma kan tsohuwar hanyar mulkin mallaka da kwasar ganima ba, ko kuma hanyar da ba ta dace ba ta neman mulkin danniya da nuna fin karfi. Haka kuma kasar Sin ba ta fitar da akidunta, ko kuma yin adawa da akida da wata kasa ba. Kasar Sin ba ta da wani shiri na maye gurbin Amurka.

Labarai Masu Nasaba

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

Haka kuma, bai dace kasar Amurka ta nemi dakile ci gaban kasar Sin da ma mamaye ta ba.

Shugaba Xi Jinping ya yi nuni da cewa, mutunta juna, da zaman tare cikin lumana, da hadin gwiwar samun nasara tare, su ne darussan da muka koya daga shekaru 50 na dangantakar kasashen Sin da Amurka, da kuma rikice-rikice tsakanin manyan kasashe a tarihi.

A Bali a shekarar da ta gabata, bangaren Amurka ya bayyana cewa, ba ya neman sauya tsarin kasar Sin, ko fara wani sabon yakin cacar baki, ko sake nuna kiyayya ga kasar Sin, ko goyon bayan ‘yancin kai na Taiwan, ko shiga rikici da kasar Sin.

A San Francisco kuma, shugaba Xi ya bayyana cewa, ya kamata kasashen Sin da Amurka su yi sabon hangen nesa tare da gina ginshiƙai biyar tare, don inganta alakar dake tsakaninsu.

Na farko, habaka daidaitacciyar fahimta tare, Na biyu, magance rashin jituwa tare yadda ya kamata. Na uku, ciyar da hadin gwiwar moriyar juna gaba tare, sai na hudu, sauke nauyin dake wuyansu a matsayinsu na manyan kasashe. Kana na biyar kuma na karshe, shi ne inganta mu’amala tsakanin al’ummomin kasashen biyu.

Shugabannin biyu sun kuma amince da kokarin da tawagoginsu ke yi na tattaunawa kan raya ka’idojin da suka shafi inganta dangantaka tsakanin kasashen biyu tun daga taron Bali.

Sun kuma jaddada muhimmancin dake akwai ga dukkan kasashen duniya, su rika mutunta juna da samun hanyar zaman tare da juna cikin lumana, da kiyaye hanyoyin tattaunawa ba tare da wata rufa-rufa ba, da magance tashe-tashen hankula, da martaba kundin tsarin mulkin MDD, da yin hadin gwiwa a fannonin cin moriyar juna, da yin takara mai tsafa a bangarorin dangantaka.

Haka kuma shugabannin biyu sun yi maraba da ci gaba da tattaunawa dangane da hakan. (Mai fassara: Ibrahim)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGanawaJoe BidenShugaban Kasar AmurkaShugaban kasar SinSinXi Jinping
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ofishin Jakadancin Saudiyya A Nijeriya Ya Yi Bayani Kan Soke Bizar Fasinjojin Nijeriya

Next Post

Ƙasashen Larabawa Da Musulmai Sun Yi Allah Wadai Da Hare-haren Isra’ila A Zirin Gaza

Related

Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 
Labarai

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

38 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

2 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Labarai

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

5 hours ago
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci
Manyan Labarai

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

7 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

8 hours ago
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu
Labarai

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

9 hours ago
Next Post
Gaza

Ƙasashen Larabawa Da Musulmai Sun Yi Allah Wadai Da Hare-haren Isra'ila A Zirin Gaza

LABARAI MASU NASABA

Boko Haram Na Yin TikTok, Suna Sarrafa Jirage Marasa Matuƙi Don Sa Ido Kan Sansanonin Soji – Bulama 

Ƙwararren Masanin Tsaro, Bulama Ya Ƙaryata Iƙirarin El-Rufai Kan Biyan ’Yan Bindiga Kuɗaɗen Fansa

September 11, 2025
Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

Wata Mahanga Ta Daban Na Kallon Ayyukan Ta’addanci

September 11, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

September 11, 2025
Najeriya: Ajandar Jagorantar Duniya Ta Ba Da Gudummawa Ga Tsarin Kasashen Duniya

Najeriya: Ajandar Jagorantar Duniya Ta Ba Da Gudummawa Ga Tsarin Kasashen Duniya

September 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

September 11, 2025
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

September 11, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

September 11, 2025
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

September 11, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

September 11, 2025
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.