ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Xi Ya Gana Da Takwaransa Na Amurka

by CMG Hausa
3 years ago
amurka

Shugaban kasar Sin Xi Jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden, sun gudanar da taron koli a rukunin gidajen alfarma na Filoli, dake birnin San Francisco na kasar Amurka jiya Laraba agogon wurin, inda suka yi musayar ra’ayoyi da ma bayanai kan muhimman batutuwa masu sarkakiya dake da muhimmanci ga alkiblar dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka, da manyan batutuwan da suka shafi zaman lafiya da ci gaban duniya.

Shugaba Xi Jinping ya bayyana cewa, ga kasashen Sin da Amurka, juya wa juna baya ba shi ne zabi ba. Ba gaskiya ba ne wani bangare ya sakewa wani bangare fasali. Kuma rikici da nuna adawa na iya haifar da sakamakon da bangarorin biyu ba za su iya jurewa ba.

Haka kuma takarar manyan kasashe, ba za ta iya magance matsalolin da ke addabar Sin da Amurka ko duniya ba. Duniya tana da girman da ƙasashen biyu za su sakata su wala, kuma nasarar wata kasa dama ce ga wata.

ADVERTISEMENT
  • Shugaba Xi Ya Isa Birnin San Francisco Don Ganawa Da Takwaransa Na Amurka Da Halartar Taron Shugabannin Mambobin Kungiyar APEC

 

Shugaban na kasar Sin ya kuma yi karin haske, kan muhimman sigogin tsarin zamanintar da kasar Sin da ma’anarsa, da ci gaban da kasar Sin ke samu, da kuma manufarta bisa manyan tsare-tsare. Ya yi nuni da cewa, kasar Sin tana kokarin farfado da al’ummar Sinawa daga dukkan fannoni ta hanyar zamanantar da kasar. Don haka, ba za ta koma kan tsohuwar hanyar mulkin mallaka da kwasar ganima ba, ko kuma hanyar da ba ta dace ba ta neman mulkin danniya da nuna fin karfi. Haka kuma kasar Sin ba ta fitar da akidunta, ko kuma yin adawa da akida da wata kasa ba. Kasar Sin ba ta da wani shiri na maye gurbin Amurka.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Haka kuma, bai dace kasar Amurka ta nemi dakile ci gaban kasar Sin da ma mamaye ta ba.

Shugaba Xi Jinping ya yi nuni da cewa, mutunta juna, da zaman tare cikin lumana, da hadin gwiwar samun nasara tare, su ne darussan da muka koya daga shekaru 50 na dangantakar kasashen Sin da Amurka, da kuma rikice-rikice tsakanin manyan kasashe a tarihi.

A Bali a shekarar da ta gabata, bangaren Amurka ya bayyana cewa, ba ya neman sauya tsarin kasar Sin, ko fara wani sabon yakin cacar baki, ko sake nuna kiyayya ga kasar Sin, ko goyon bayan ‘yancin kai na Taiwan, ko shiga rikici da kasar Sin.

A San Francisco kuma, shugaba Xi ya bayyana cewa, ya kamata kasashen Sin da Amurka su yi sabon hangen nesa tare da gina ginshiƙai biyar tare, don inganta alakar dake tsakaninsu.

Na farko, habaka daidaitacciyar fahimta tare, Na biyu, magance rashin jituwa tare yadda ya kamata. Na uku, ciyar da hadin gwiwar moriyar juna gaba tare, sai na hudu, sauke nauyin dake wuyansu a matsayinsu na manyan kasashe. Kana na biyar kuma na karshe, shi ne inganta mu’amala tsakanin al’ummomin kasashen biyu.

Shugabannin biyu sun kuma amince da kokarin da tawagoginsu ke yi na tattaunawa kan raya ka’idojin da suka shafi inganta dangantaka tsakanin kasashen biyu tun daga taron Bali.

Sun kuma jaddada muhimmancin dake akwai ga dukkan kasashen duniya, su rika mutunta juna da samun hanyar zaman tare da juna cikin lumana, da kiyaye hanyoyin tattaunawa ba tare da wata rufa-rufa ba, da magance tashe-tashen hankula, da martaba kundin tsarin mulkin MDD, da yin hadin gwiwa a fannonin cin moriyar juna, da yin takara mai tsafa a bangarorin dangantaka.

Haka kuma shugabannin biyu sun yi maraba da ci gaba da tattaunawa dangane da hakan. (Mai fassara: Ibrahim)

amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Gaza

Ƙasashen Larabawa Da Musulmai Sun Yi Allah Wadai Da Hare-haren Isra'ila A Zirin Gaza

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.