ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙasashen Larabawa Da Musulmai Sun Yi Allah Wadai Da Hare-haren Isra’ila A Zirin Gaza

by Sulaiman
3 years ago
Gaza

Taron Haɗin Guiwar Ƙasashen Larabawa da sauran ƙasashen Musulmai, ya yi tir tare da nuna rashin amincewa kan hare-haren da sojojin Isra’ila ke ci gaba da kaiwa a Gaza.

Taron wanda aka gudanar ranar Asabar, 11 ga Nuwamba, ya bayyana cewa abin da sojojin Isra’ila suka yi laifin tsallake ƙa’idoji da sharuɗɗan yaƙi ne, kuma dabbanci ne kan Falasɗinawa fararen hula.

  • Tattalin Arzikin Sin Na Kan Hanyar Kai Kasar Ga Cimma Burikanta Na 2023
  • Hukumar Kwastam Ta Kama Kwayoyin Tramadol Na Biliyan N3.55bn A Legas

Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris ne ya tabbatar da haka, a cikin wata sanarwar da Jami’in Yaɗa Labarai na ministan, Rabi’u Ibrahim ya fitar.

ADVERTISEMENT

Idris, wanda ya na cikin tawagar Shugaban Ƙasa Bola Tinubu a wurin taron, ya ƙara da cewa, an kuma yi kira da a gaggauta gudanar da gagarimin taron duniya, inda za a bijiro da hanyoyin tabbatar da wanzuwar zaman lafiya a yankin Falasɗinu.

Sanarwar bayan taron da wanda shugabannin ƙasashen Ƙungiyar OIC da na Majalisar Ƙasashen Larabawa suka halarta, an yi kira da a gaggauta tsagaita dukkan hare-haren da sojojin Isra’ila ke kaiwa a yankin Gaza.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Kuma sun fito ƙarara sun ce farmakin da Isra’ila ke kaiwa kan Gaza ci gaba ne da irin mamayar da ta yi wa Falasɗinawa a 1967 a yankin Gaza, West Bank, Al-Quds Al-Sharif da kuma Arewacin Jerusalem.

Sannan kuma taron ya buƙaci Majalisar Ɗinkin Duniya ta fito da ƙwaƙƙwarar matsaya a ƙarƙashin Majalisar Tsaro ta Majalisar Ɗinkin, wadda za ta tilasta daina duk wani nau’i da salo na gallazawa da Isra’ila ke yi wa Falasɗinawa.

Haka nan kuma wannan taro ya nemi Isra’ila ta kawo ƙarshen mamayar da ta ke yi a yankin, domin ya karya ƙa’ida da iyakokin da dokokin ƙasa da ƙasa suka shar’anta.

Sun ce musamman farmakin ya saɓa wa ƙa’idar Majalisar Ɗinkin Duniya mai lamba AES-101.25, ta ranar 26 ga Oktoba, 2013.

A wurin taron, shugabannin sun yi kakkausan kira ga Majalisar Tsaro ta Majalisar Ɗinkin Duniya cewa “ta gaggauta yin Allah-wadai da dabbacin da sojojin Isra’ila ke kan yi na ruguza asibitoci a Zirin Gaza. Kuma ta yi tir kan hana a shigar wa Falasɗinawa da magunguna, abinci fetur da katse wutar lantarkin da mahukuntan Isra’ila ɗin suka yi a Zirin Gaza.”

An zartas da cewa matuƙar Majalisar Ɗinkin Duniya ta ƙi yin tir da dabbancin da sojojin Isra’ila ke aikatawa a Zirin Gaza, to tamkar ta halasta mummunan kisan da ake wa fararen hula ne da suka ƙunshi ƙananan yara, dattawa, mata da kuma ruguza Gaza da ake kan yi.

Sun ce ya zama wajibi Isra’ila ta ɗage takunkumin datse Zirin Gaza da ta yi, tsawon shekaru masu yawa.

Sannan kuma taron ya yi tir dangane da yadda wasu ƙasashe suka riƙa taimaka wa Isra’ila da muggan makaman da take amfani da su, ta na kisan gilla kan Falasɗinawa, tare da ruguza masu gidaje, asibitoci, makarantu, masallatai, coci-coci da sauran wuraren more rayuwa.

Gaza
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya
  • Sulaiman
    Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari
  • Sulaiman
    Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
Gobara

Gobara Ta Kone Fiye Da Masaukai Dubu A Sansanin Gudun Hijira Na Borno

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.