• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Xi Ya Jagoranci Taron Karawa Juna Sani Game Da Bunkasa Ci Gaban Yankin Yammacin Kasar 

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaba Xi Ya Jagoranci Taron Karawa Juna Sani Game Da Bunkasa Ci Gaban Yankin Yammacin Kasar 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin yau Talata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jagoranci wani taron karawa juna sani a birnin Chongqing dake kudu maso yammacin kasar, game da bunkasa ci gaban yankin yammacin kasar Sin a sabon zamani.

Cikin muhimmin jawabin da ya gabatar yayin zaman, shugaba Xi ya jaddada cewa, yankin yammacin kasar Sin na taka muhimmiyar rawa, wajen yin gyare-gyare a kasar da samun ci gaba da kuma daidaito.

  • Sin Ta Kalubalanci Amurka Da Ta Dubi Kanta Game Da Yanayin Kare Hakkin Dan Adam
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai 2 A Kaduna

Ya ce, wajibi ne a aiwatar da manufofi, da matakan kwamitin kolin JKS, ta fuskar ingiza ci gaban yankin na yammacin Sin, kana a kara kafa wani sabon salo na kare kai, da kara bude kofa ga ketare, da samun ci gaba mai inganci, da bunkasa daukacin karfi, da kwarewar bunkasa kai mai dorewa na yankin, a kuma kara azamar bude sabon babi na bunkasa yankin na yammacin Sin, karkashin burin zamanantarwa irin na kasar Sin.

Xi Jinping ya yi rangadi a birnin Chongqing daga jiya Litinin zuwa yau Talata. Yayin rangadin, Xi ya kai ziyarar cibiyar jigilar kayayyaki ta kasa da kasa, da unguwar mazauna dake yankin Jiulongpo, da kuma cibiyar tafiyar da harkokin birnin ta zamani.

Ya kuma gano kokarin da gwamnatin birnin ke yi wajen gaggauta raya sabuwar cibiyar cinikayya daga kan tudu zuwa teku ta kasa da kasa dake yammacin kasar, da aiwatar da ayyukan sabunta birnin, da tabbatar da kyautata rayuwar jama’a, da ma yunkurin zamanantar da tsarin tafiyar da harkokin birnin.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Kana shugaba Xi Jinping ya ce, walwalar jama’a abu ne mai matukar muhimmanci ga zamanantar da kasar Sin, manufar JKS ita ce, tabbatar da jama’a suna rayuwa cikin farin ciki.

Xi Jinping ya kuma jaddada cewa, ya zama wajibi a fayyace iko da nauyin da ya rataya a wuyan wadanda suke aiki a matakin farko, domin rage masu nauyi.

Shugaban ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci wata unguwa dake yankin Jiulongpo, wadda aka yi wa gyaran fuska kuma take cikin yanayi mai kyau.

Haka kuma, ya ziyarci cibiyar kula da harkokin unguwar, yana mai tambayar ma’aikata ayyukan da suke gudanarwa da albashinsu da yawan ayyukansu, domin fahimtar yadda yunkurin ragewa ma’aikata yawan ayyuka a matakin unguwanni ke yin tasiri a shekarun baya-bayan nan. (Fa’iza Mustapha&Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Fitar Da Miliyan 309.5 Don Tallafawa Ɗaliban Da Ke Karatu a Ƙasashen waje 

Next Post

Yadda Sojoji Suka Fatattaki ‘Yan Bindiga Tare Da Ceto Mutane 5 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

Related

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

12 hours ago
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika
Daga Birnin Sin

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

13 hours ago
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

14 hours ago
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

15 hours ago
Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki
Daga Birnin Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

16 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

17 hours ago
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 11, Sun Rusa Sansanoni A Dajin Sambisa

Yadda Sojoji Suka Fatattaki 'Yan Bindiga Tare Da Ceto Mutane 5 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.