• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Xi Ya Jagoranci Taron Karawa Juna Sani Game Da Bunkasa Ci Gaban Yankin Yammacin Kasar 

by CGTN Hausa
2 years ago
Xi

Da yammacin yau Talata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jagoranci wani taron karawa juna sani a birnin Chongqing dake kudu maso yammacin kasar, game da bunkasa ci gaban yankin yammacin kasar Sin a sabon zamani.

Cikin muhimmin jawabin da ya gabatar yayin zaman, shugaba Xi ya jaddada cewa, yankin yammacin kasar Sin na taka muhimmiyar rawa, wajen yin gyare-gyare a kasar da samun ci gaba da kuma daidaito.

  • Sin Ta Kalubalanci Amurka Da Ta Dubi Kanta Game Da Yanayin Kare Hakkin Dan Adam
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai 2 A Kaduna

Ya ce, wajibi ne a aiwatar da manufofi, da matakan kwamitin kolin JKS, ta fuskar ingiza ci gaban yankin na yammacin Sin, kana a kara kafa wani sabon salo na kare kai, da kara bude kofa ga ketare, da samun ci gaba mai inganci, da bunkasa daukacin karfi, da kwarewar bunkasa kai mai dorewa na yankin, a kuma kara azamar bude sabon babi na bunkasa yankin na yammacin Sin, karkashin burin zamanantarwa irin na kasar Sin.

Xi Jinping ya yi rangadi a birnin Chongqing daga jiya Litinin zuwa yau Talata. Yayin rangadin, Xi ya kai ziyarar cibiyar jigilar kayayyaki ta kasa da kasa, da unguwar mazauna dake yankin Jiulongpo, da kuma cibiyar tafiyar da harkokin birnin ta zamani.

Ya kuma gano kokarin da gwamnatin birnin ke yi wajen gaggauta raya sabuwar cibiyar cinikayya daga kan tudu zuwa teku ta kasa da kasa dake yammacin kasar, da aiwatar da ayyukan sabunta birnin, da tabbatar da kyautata rayuwar jama’a, da ma yunkurin zamanantar da tsarin tafiyar da harkokin birnin.

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Kana shugaba Xi Jinping ya ce, walwalar jama’a abu ne mai matukar muhimmanci ga zamanantar da kasar Sin, manufar JKS ita ce, tabbatar da jama’a suna rayuwa cikin farin ciki.

Xi Jinping ya kuma jaddada cewa, ya zama wajibi a fayyace iko da nauyin da ya rataya a wuyan wadanda suke aiki a matakin farko, domin rage masu nauyi.

Shugaban ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci wata unguwa dake yankin Jiulongpo, wadda aka yi wa gyaran fuska kuma take cikin yanayi mai kyau.

Haka kuma, ya ziyarci cibiyar kula da harkokin unguwar, yana mai tambayar ma’aikata ayyukan da suke gudanarwa da albashinsu da yawan ayyukansu, domin fahimtar yadda yunkurin ragewa ma’aikata yawan ayyuka a matakin unguwanni ke yin tasiri a shekarun baya-bayan nan. (Fa’iza Mustapha&Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 11, Sun Rusa Sansanoni A Dajin Sambisa

Yadda Sojoji Suka Fatattaki 'Yan Bindiga Tare Da Ceto Mutane 5 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

Xi Jinping Zai Gana Da Donald Trump

October 29, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Kama Wani Matashi Da Ya Yi Kira A Yi Juyin Mulki A Kafofin Sada Zumunta

October 29, 2025
An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.