ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaba Xi Ya Jagoranci Taron Karawa Juna Sani Game Da Bunkasa Ci Gaban Yankin Yammacin Kasar 

by CGTN Hausa
2 years ago
Xi

Da yammacin yau Talata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya jagoranci wani taron karawa juna sani a birnin Chongqing dake kudu maso yammacin kasar, game da bunkasa ci gaban yankin yammacin kasar Sin a sabon zamani.

Cikin muhimmin jawabin da ya gabatar yayin zaman, shugaba Xi ya jaddada cewa, yankin yammacin kasar Sin na taka muhimmiyar rawa, wajen yin gyare-gyare a kasar da samun ci gaba da kuma daidaito.

  • Sin Ta Kalubalanci Amurka Da Ta Dubi Kanta Game Da Yanayin Kare Hakkin Dan Adam
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai 2 A Kaduna

Ya ce, wajibi ne a aiwatar da manufofi, da matakan kwamitin kolin JKS, ta fuskar ingiza ci gaban yankin na yammacin Sin, kana a kara kafa wani sabon salo na kare kai, da kara bude kofa ga ketare, da samun ci gaba mai inganci, da bunkasa daukacin karfi, da kwarewar bunkasa kai mai dorewa na yankin, a kuma kara azamar bude sabon babi na bunkasa yankin na yammacin Sin, karkashin burin zamanantarwa irin na kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Xi Jinping ya yi rangadi a birnin Chongqing daga jiya Litinin zuwa yau Talata. Yayin rangadin, Xi ya kai ziyarar cibiyar jigilar kayayyaki ta kasa da kasa, da unguwar mazauna dake yankin Jiulongpo, da kuma cibiyar tafiyar da harkokin birnin ta zamani.

Ya kuma gano kokarin da gwamnatin birnin ke yi wajen gaggauta raya sabuwar cibiyar cinikayya daga kan tudu zuwa teku ta kasa da kasa dake yammacin kasar, da aiwatar da ayyukan sabunta birnin, da tabbatar da kyautata rayuwar jama’a, da ma yunkurin zamanantar da tsarin tafiyar da harkokin birnin.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Kana shugaba Xi Jinping ya ce, walwalar jama’a abu ne mai matukar muhimmanci ga zamanantar da kasar Sin, manufar JKS ita ce, tabbatar da jama’a suna rayuwa cikin farin ciki.

Xi Jinping ya kuma jaddada cewa, ya zama wajibi a fayyace iko da nauyin da ya rataya a wuyan wadanda suke aiki a matakin farko, domin rage masu nauyi.

Shugaban ya bayyana haka ne lokacin da ya ziyarci wata unguwa dake yankin Jiulongpo, wadda aka yi wa gyaran fuska kuma take cikin yanayi mai kyau.

Haka kuma, ya ziyarci cibiyar kula da harkokin unguwar, yana mai tambayar ma’aikata ayyukan da suke gudanarwa da albashinsu da yawan ayyukansu, domin fahimtar yadda yunkurin ragewa ma’aikata yawan ayyuka a matakin unguwanni ke yin tasiri a shekarun baya-bayan nan. (Fa’iza Mustapha&Saminu Alhassan)

Xi
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

MASU ALAKA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
Daga Birnin Sin

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’addar ISWAP 11, Sun Rusa Sansanoni A Dajin Sambisa

Yadda Sojoji Suka Fatattaki 'Yan Bindiga Tare Da Ceto Mutane 5 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

June 27, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

June 27, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

June 27, 2026
Xi

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

June 27, 2026
Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

Yadda Aka Kama Manyan Kwamandojin Boko Haram 7 Suna Dawowa Daga Aikin Hajji

June 27, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji

June 27, 2026
Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.