ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Kalubalanci Amurka Da Ta Dubi Kanta Game Da Yanayin Kare Hakkin Dan Adam

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Game da rahoton da ma’aikatar harkokin wajen kasar Amurka ta gabatar don gane da batun kare hakkin dan Adam na kasa da kasa, wanda ya zargi sauran kasashe da gazawa wajen kare hakkin dan Adam, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau cewa, rahoton na Amurka, ya zargi yanayin kare hakkin dan Adam na kasashe da yankuna kimanin 200 na duniya, amma bai ambato ita kanta Amurka ba. Don haka Sin ta kalubalanci Amurka, da ta dubi kanta, ta fara da warware matsalarta a wannan fanni.

Wang Wenbin ya bayyana cewa, Amurka na gabatar da rahoton kare hakkin dan Adam na shekara-shekara, amma abubuwan dake shafar kasar Sin a rahoton jita-jita ne kawai domin kulle-kullen siyasa, matakin da Sin din ba za ta amince da shi ba.

  • Kasar Sin Ta Bayyana Tarin Rarar Da Take Da Shi Ta Albarkartun Mai Da Iskar Gas
  • Jami’in Ma’aikatar Wajen Sin Ya Yi Tsokaci Game Da Ziyarar Sakataren Wajen Amurka A Kasar

Har ila yau, Wang Wenbin ya yi nuni da cewa, idan Amurka na matukar mai da hankali ga kare hakkin dan Adam, to kamata ya yi ta daidaita matsalolin bindigogi, da miyagun kwayoyi, da nuna bambancin launin fata, da keta hakkin dan Adam dake faruwa a kasar, kana ta yi la’akari da matsalolin da ta kawo wa yankuna masu fama da rigingimu, ta hanyar tsoma baki, da samar da makamai, da kuma ta da zaune-tsaye.

ADVERTISEMENT

Ban da wannan kuma, Wang Wenbin ya ce, Sin na fatan Amurka za ta dakatar da rura wutar rikici, ko bata sunan wasu sassa don gane da batun Ukraine, domin hakan ba zai warware rikicin da kasar ke fama da shi ba.

Wang, ya yi tsokacin ne yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa na yau Talata, lokacin da yake amsa tambayoyi game da wasu rahotanni daga bangaren Amurka, masu kunshe da zargin alakar tattalin arziki da musaya tsakanin Sin da kasar Rasha. Game da hakan, Wang Wenbin ya ce, yayin da Amurka ke samar da tarin tallafi ga Ukraine, a daya bangaren ba gaira ba dalili, ta soki halastacciyar musayar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Rasha. Ya ce, “Yin hakan munafurci ne da rashin sanin ya kamata, kuma Sin na matukar adawa da hakan”.

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Bugu da kari, Wang Wenbin ya yi tsokaci game da wasu rahotanni da suka fito daga kasashen Jamus da Birtaniya, game da zargin nan da wasu sassa ke yi wa kasar Sin, na “Barazanar Leken Asiri”. Yayin taron manema labarai na Talatar nan, Wang Wenbin ya ce, ko shakka babu, burin masu zarge-zargen shi ne bata sunan kasar Sin, da dakile kamfanonin kasar, da gurgunta yanayin hadin gwiwa tsakanin Sin da Turai. Kasar Sin na kira ga sassa masu ruwa da tsaki a wannan batu, da su kauracewa wannan manufa ta kulle-kullen siyasa na shafawa kasar Sin bakin fenti.(Zainab Zhang&Saminu Alhassan)

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Japan Ta Kwaye Lullubin Da Take Fakewa Da Shi Wajen Kiran Kanta Mai Kaunar Zaman Lafiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Yanayin Bunkasar Hada-hadar Cinikayyar Sin Ya Shaida Karkon Manufofin Raya Tattalin Arzikin Kasar
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Shaida Gamsuwar Masu Bayyana Ra’ayoyi Da Gudunmawar Sin Game Da Tsarin Jagorancin Hakkin Bil’adama
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Kasar Sin Ta Sanar Da Sanya Takunkumi A Kan Ministan Tsaron Kasar Philippines Da Iyalansa

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Fitar Da Miliyan 309.5 Don Tallafawa Ɗaliban Da Ke Karatu a Ƙasashen waje 

Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Fitar Da Miliyan 309.5 Don Tallafawa Ɗaliban Da Ke Karatu a Ƙasashen waje 

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.