• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Ta 2025

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Ta 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A gabannin shekara ta 2025, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da jawabin murnar shiga sabuwar shekara, ta kafar babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG da kafar sadarwar intanet, inda ya takaita wasu muhimman abubuwan da suka wakana a kasar Sin da ma duniya baki daya a shekarar dake karewa wato 2024, tare da yi wa kowa fatan cimma burinsa, da samun walwala da zaman jin dadi da kwanciyar hankali.

Xi Jinping ya siffanta shekara ta 2024 da mai cike da abubuwan burgewa, da abubuwan da ba za’a iya mantawa da su ba, da jimloli biyu, wato “mun wuce yanayin bazara, da yanayin zafi, da yanayin kaka, da kuma yanayin hunturu tare, kuma mun haye wahalhalu da cimma nasarori tare”, inda kuma ya yi amfani da wasu alkaluma guda uku don shaida nasarorin da kasarsa ta samu a wannan shekara. Na farko, bisa hasashen da aka yi, jimillar GDPn kasar zai zarce kudin Sin Yuan tiriliyan 130, al’amarin da ya nuna murmurewar tattalin arzikin kasar. Na biyu shi ne, yawan hatsin da aka samu a dukkanin fadin kasar Sin ya wuce kilogiram biliyan 700, al’amarin da ya sa al’ummar kasar suka kara samun abinci. Na uku kuwa shi ne, yawan motoci dake aiki da sabbin makamashi da kasar ta kera ya zarce miliyan 10, al’amarin da ya shaida bullar wasu sabbin sana’o’i da ayyuka da salo.

  • Dabaru Irin Na Sin A Kan Daidaita Harkokin Duniya A 2024
  • Sin Ta Kafa Manya Da Matsakaitan Yankunan Ban Ruwa 7,300

Shugaba Xi ya kuma ayyana ziyarce-ziyarcen da ya yi a cikin kasar Sin a shekara ta 2024, inda ya nuna jin dadi sosai, ganin yadda al’ummar kasar ke morewa, gami da nuna gamsuwa ga rayuwarsu. Xi ya ce, duk yadda wani abu yake shafar wani iyali, ko wata kasa, ko kuma sassan kasa da kasa, yadda al’umma za su ji dadin zaman rayuwarsu shi ne muhimmin aiki na farko da kasar Sin take sanyawa a gaban komai.

Game da halin da ake ciki a duk duniya, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, duniya na fuskantar sauye-sauye da rikice-rikice a halin yanzu, kuma a matsayinta na babbar kasa dake daukar nauyi a wuyanta, Sin na himmatuwa wajen kawo sauye-sauye ga tsarin tafiyar da harkokin duniya, da zurfafa hadin-gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Kuma tana kokarin zurfafawa, gami da inganta ayyukan da suka shafi shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, da gudanar da taron koli na Beijing na dandalin tattauna hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka wato FOCAC cikin nasara. A wasu taruka dake kunshe da bangarori biyu, ko kuma bangarori da dama, kasar Sin ta bullo da manufofinta na hakika, domin kara sanya kuzari ga tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk fadin duniya.

Shugaba Xi yana cike da imani a yayin da yake hangen nesa ga shekara mai kamawa wato 2025, inda ya ce, a shekara ta 2025, kasarsa za ta kammala shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 14, kuma yadda ake kokarin aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga ketare, tabbas zai samar da kyakkyawar makoma ga ayyukan zamanintar da kasar Sin. Kaza lika, kasar Sin za ta kara kyautata ayyukan raya zaman al’umma, da daidaita batutuwa manya da kanana na al’umma, ta yadda kowa zai kara farin ciki da walwala.

Labarai Masu Nasaba

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Shugaba Xi ya ce, yayin da ake gaggauta samun manyan sauye-sauyen yanayin da ake ciki a duniya, kamata ya yi sassan kasa da kasa su kai zuciya nesa, su mai da hankali a kan makomar dan Adam. Kasar Sin na son yin kokari tare da sassan kasa da kasa, wajen zama masu hadin gwiwar sada zumunta da juna, masu sa kaimin musayar wayewar kai, kuma masu gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam, don samar da kyakkyawar makomar duniya. (Murtala Zhang&Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Fashi 40, Sun Ceto Mutum 319 A 2024

Next Post

Kwamitin Kasa Na Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ya Yi Bikin Maraba Da Sabuwar Shekara

Related

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya
Daga Birnin Sin

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

20 hours ago
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
Daga Birnin Sin

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

21 hours ago
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

22 hours ago
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing
Daga Birnin Sin

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

23 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

2 days ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

2 days ago
Next Post
Kwamitin Kasa Na Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ya Yi Bikin Maraba Da Sabuwar Shekara

Kwamitin Kasa Na Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ya Yi Bikin Maraba Da Sabuwar Shekara

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.