• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Ta 2025

by CGTN Hausa and Sulaiman
5 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Ta 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A gabannin shekara ta 2025, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da jawabin murnar shiga sabuwar shekara, ta kafar babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG da kafar sadarwar intanet, inda ya takaita wasu muhimman abubuwan da suka wakana a kasar Sin da ma duniya baki daya a shekarar dake karewa wato 2024, tare da yi wa kowa fatan cimma burinsa, da samun walwala da zaman jin dadi da kwanciyar hankali.

Xi Jinping ya siffanta shekara ta 2024 da mai cike da abubuwan burgewa, da abubuwan da ba za’a iya mantawa da su ba, da jimloli biyu, wato “mun wuce yanayin bazara, da yanayin zafi, da yanayin kaka, da kuma yanayin hunturu tare, kuma mun haye wahalhalu da cimma nasarori tare”, inda kuma ya yi amfani da wasu alkaluma guda uku don shaida nasarorin da kasarsa ta samu a wannan shekara. Na farko, bisa hasashen da aka yi, jimillar GDPn kasar zai zarce kudin Sin Yuan tiriliyan 130, al’amarin da ya nuna murmurewar tattalin arzikin kasar. Na biyu shi ne, yawan hatsin da aka samu a dukkanin fadin kasar Sin ya wuce kilogiram biliyan 700, al’amarin da ya sa al’ummar kasar suka kara samun abinci. Na uku kuwa shi ne, yawan motoci dake aiki da sabbin makamashi da kasar ta kera ya zarce miliyan 10, al’amarin da ya shaida bullar wasu sabbin sana’o’i da ayyuka da salo.

  • Dabaru Irin Na Sin A Kan Daidaita Harkokin Duniya A 2024
  • Sin Ta Kafa Manya Da Matsakaitan Yankunan Ban Ruwa 7,300

Shugaba Xi ya kuma ayyana ziyarce-ziyarcen da ya yi a cikin kasar Sin a shekara ta 2024, inda ya nuna jin dadi sosai, ganin yadda al’ummar kasar ke morewa, gami da nuna gamsuwa ga rayuwarsu. Xi ya ce, duk yadda wani abu yake shafar wani iyali, ko wata kasa, ko kuma sassan kasa da kasa, yadda al’umma za su ji dadin zaman rayuwarsu shi ne muhimmin aiki na farko da kasar Sin take sanyawa a gaban komai.

Game da halin da ake ciki a duk duniya, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, duniya na fuskantar sauye-sauye da rikice-rikice a halin yanzu, kuma a matsayinta na babbar kasa dake daukar nauyi a wuyanta, Sin na himmatuwa wajen kawo sauye-sauye ga tsarin tafiyar da harkokin duniya, da zurfafa hadin-gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Kuma tana kokarin zurfafawa, gami da inganta ayyukan da suka shafi shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, da gudanar da taron koli na Beijing na dandalin tattauna hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka wato FOCAC cikin nasara. A wasu taruka dake kunshe da bangarori biyu, ko kuma bangarori da dama, kasar Sin ta bullo da manufofinta na hakika, domin kara sanya kuzari ga tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk fadin duniya.

Shugaba Xi yana cike da imani a yayin da yake hangen nesa ga shekara mai kamawa wato 2025, inda ya ce, a shekara ta 2025, kasarsa za ta kammala shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 14, kuma yadda ake kokarin aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga ketare, tabbas zai samar da kyakkyawar makoma ga ayyukan zamanintar da kasar Sin. Kaza lika, kasar Sin za ta kara kyautata ayyukan raya zaman al’umma, da daidaita batutuwa manya da kanana na al’umma, ta yadda kowa zai kara farin ciki da walwala.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Shugaba Xi ya ce, yayin da ake gaggauta samun manyan sauye-sauyen yanayin da ake ciki a duniya, kamata ya yi sassan kasa da kasa su kai zuciya nesa, su mai da hankali a kan makomar dan Adam. Kasar Sin na son yin kokari tare da sassan kasa da kasa, wajen zama masu hadin gwiwar sada zumunta da juna, masu sa kaimin musayar wayewar kai, kuma masu gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam, don samar da kyakkyawar makomar duniya. (Murtala Zhang&Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Fashi 40, Sun Ceto Mutum 319 A 2024

Next Post

Kwamitin Kasa Na Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ya Yi Bikin Maraba Da Sabuwar Shekara

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

2 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

4 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

4 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

21 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

21 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

23 hours ago
Next Post
Kwamitin Kasa Na Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ya Yi Bikin Maraba Da Sabuwar Shekara

Kwamitin Kasa Na Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ya Yi Bikin Maraba Da Sabuwar Shekara

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Xi Jinping

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.