• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Ta 2025

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Ta 2025
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A gabannin shekara ta 2025, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da jawabin murnar shiga sabuwar shekara, ta kafar babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG da kafar sadarwar intanet, inda ya takaita wasu muhimman abubuwan da suka wakana a kasar Sin da ma duniya baki daya a shekarar dake karewa wato 2024, tare da yi wa kowa fatan cimma burinsa, da samun walwala da zaman jin dadi da kwanciyar hankali.

Xi Jinping ya siffanta shekara ta 2024 da mai cike da abubuwan burgewa, da abubuwan da ba za’a iya mantawa da su ba, da jimloli biyu, wato “mun wuce yanayin bazara, da yanayin zafi, da yanayin kaka, da kuma yanayin hunturu tare, kuma mun haye wahalhalu da cimma nasarori tare”, inda kuma ya yi amfani da wasu alkaluma guda uku don shaida nasarorin da kasarsa ta samu a wannan shekara. Na farko, bisa hasashen da aka yi, jimillar GDPn kasar zai zarce kudin Sin Yuan tiriliyan 130, al’amarin da ya nuna murmurewar tattalin arzikin kasar. Na biyu shi ne, yawan hatsin da aka samu a dukkanin fadin kasar Sin ya wuce kilogiram biliyan 700, al’amarin da ya sa al’ummar kasar suka kara samun abinci. Na uku kuwa shi ne, yawan motoci dake aiki da sabbin makamashi da kasar ta kera ya zarce miliyan 10, al’amarin da ya shaida bullar wasu sabbin sana’o’i da ayyuka da salo.

  • Dabaru Irin Na Sin A Kan Daidaita Harkokin Duniya A 2024
  • Sin Ta Kafa Manya Da Matsakaitan Yankunan Ban Ruwa 7,300

Shugaba Xi ya kuma ayyana ziyarce-ziyarcen da ya yi a cikin kasar Sin a shekara ta 2024, inda ya nuna jin dadi sosai, ganin yadda al’ummar kasar ke morewa, gami da nuna gamsuwa ga rayuwarsu. Xi ya ce, duk yadda wani abu yake shafar wani iyali, ko wata kasa, ko kuma sassan kasa da kasa, yadda al’umma za su ji dadin zaman rayuwarsu shi ne muhimmin aiki na farko da kasar Sin take sanyawa a gaban komai.

Game da halin da ake ciki a duk duniya, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, duniya na fuskantar sauye-sauye da rikice-rikice a halin yanzu, kuma a matsayinta na babbar kasa dake daukar nauyi a wuyanta, Sin na himmatuwa wajen kawo sauye-sauye ga tsarin tafiyar da harkokin duniya, da zurfafa hadin-gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Kuma tana kokarin zurfafawa, gami da inganta ayyukan da suka shafi shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, da gudanar da taron koli na Beijing na dandalin tattauna hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka wato FOCAC cikin nasara. A wasu taruka dake kunshe da bangarori biyu, ko kuma bangarori da dama, kasar Sin ta bullo da manufofinta na hakika, domin kara sanya kuzari ga tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk fadin duniya.

Shugaba Xi yana cike da imani a yayin da yake hangen nesa ga shekara mai kamawa wato 2025, inda ya ce, a shekara ta 2025, kasarsa za ta kammala shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 14, kuma yadda ake kokarin aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga ketare, tabbas zai samar da kyakkyawar makoma ga ayyukan zamanintar da kasar Sin. Kaza lika, kasar Sin za ta kara kyautata ayyukan raya zaman al’umma, da daidaita batutuwa manya da kanana na al’umma, ta yadda kowa zai kara farin ciki da walwala.

Labarai Masu Nasaba

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Shugaba Xi ya ce, yayin da ake gaggauta samun manyan sauye-sauyen yanayin da ake ciki a duniya, kamata ya yi sassan kasa da kasa su kai zuciya nesa, su mai da hankali a kan makomar dan Adam. Kasar Sin na son yin kokari tare da sassan kasa da kasa, wajen zama masu hadin gwiwar sada zumunta da juna, masu sa kaimin musayar wayewar kai, kuma masu gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam, don samar da kyakkyawar makomar duniya. (Murtala Zhang&Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Fashi 40, Sun Ceto Mutum 319 A 2024

Next Post

Kwamitin Kasa Na Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ya Yi Bikin Maraba Da Sabuwar Shekara

Related

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

14 hours ago
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya
Daga Birnin Sin

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

15 hours ago
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO
Daga Birnin Sin

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

16 hours ago
Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire
Daga Birnin Sin

Dorad Da Zuba Jari A Sashen Bincike Da Samarwa Da Kare Ikon Mallaka Sun Taimaka Wa Sin Zama Kan Gaba A Duniya Ta Fuskar Kirkire-kirkire

17 hours ago
Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 
Daga Birnin Sin

Jami’ar IMF Ta Yaba Da Kwararan Bayanan Tattalin Arziki Da Manufofin Kasafin Kudi Na Kasar Sin 

18 hours ago
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha
Daga Birnin Sin

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Zaman Kwamitin Sada Zumunta Da Zaman Lafiya Da Ci Gaba Tsakanin Sin Da Rasha

19 hours ago
Next Post
Kwamitin Kasa Na Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ya Yi Bikin Maraba Da Sabuwar Shekara

Kwamitin Kasa Na Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ya Yi Bikin Maraba Da Sabuwar Shekara

LABARAI MASU NASABA

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.