ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gabatar Da Jawabin Murnar Shiga Sabuwar Shekara Ta 2025

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Xi Jinping

A gabannin shekara ta 2025, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da jawabin murnar shiga sabuwar shekara, ta kafar babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG da kafar sadarwar intanet, inda ya takaita wasu muhimman abubuwan da suka wakana a kasar Sin da ma duniya baki daya a shekarar dake karewa wato 2024, tare da yi wa kowa fatan cimma burinsa, da samun walwala da zaman jin dadi da kwanciyar hankali.

Xi Jinping ya siffanta shekara ta 2024 da mai cike da abubuwan burgewa, da abubuwan da ba za’a iya mantawa da su ba, da jimloli biyu, wato “mun wuce yanayin bazara, da yanayin zafi, da yanayin kaka, da kuma yanayin hunturu tare, kuma mun haye wahalhalu da cimma nasarori tare”, inda kuma ya yi amfani da wasu alkaluma guda uku don shaida nasarorin da kasarsa ta samu a wannan shekara. Na farko, bisa hasashen da aka yi, jimillar GDPn kasar zai zarce kudin Sin Yuan tiriliyan 130, al’amarin da ya nuna murmurewar tattalin arzikin kasar. Na biyu shi ne, yawan hatsin da aka samu a dukkanin fadin kasar Sin ya wuce kilogiram biliyan 700, al’amarin da ya sa al’ummar kasar suka kara samun abinci. Na uku kuwa shi ne, yawan motoci dake aiki da sabbin makamashi da kasar ta kera ya zarce miliyan 10, al’amarin da ya shaida bullar wasu sabbin sana’o’i da ayyuka da salo.

  • Dabaru Irin Na Sin A Kan Daidaita Harkokin Duniya A 2024
  • Sin Ta Kafa Manya Da Matsakaitan Yankunan Ban Ruwa 7,300

Shugaba Xi ya kuma ayyana ziyarce-ziyarcen da ya yi a cikin kasar Sin a shekara ta 2024, inda ya nuna jin dadi sosai, ganin yadda al’ummar kasar ke morewa, gami da nuna gamsuwa ga rayuwarsu. Xi ya ce, duk yadda wani abu yake shafar wani iyali, ko wata kasa, ko kuma sassan kasa da kasa, yadda al’umma za su ji dadin zaman rayuwarsu shi ne muhimmin aiki na farko da kasar Sin take sanyawa a gaban komai.

ADVERTISEMENT

Game da halin da ake ciki a duk duniya, shugaba Xi ya yi nuni da cewa, duniya na fuskantar sauye-sauye da rikice-rikice a halin yanzu, kuma a matsayinta na babbar kasa dake daukar nauyi a wuyanta, Sin na himmatuwa wajen kawo sauye-sauye ga tsarin tafiyar da harkokin duniya, da zurfafa hadin-gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Kuma tana kokarin zurfafawa, gami da inganta ayyukan da suka shafi shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, da gudanar da taron koli na Beijing na dandalin tattauna hadin gwiwar kasar Sin da kasashen Afirka wato FOCAC cikin nasara. A wasu taruka dake kunshe da bangarori biyu, ko kuma bangarori da dama, kasar Sin ta bullo da manufofinta na hakika, domin kara sanya kuzari ga tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk fadin duniya.

Shugaba Xi yana cike da imani a yayin da yake hangen nesa ga shekara mai kamawa wato 2025, inda ya ce, a shekara ta 2025, kasarsa za ta kammala shirin raya kasa na shekaru biyar biyar karo na 14, kuma yadda ake kokarin aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga ketare, tabbas zai samar da kyakkyawar makoma ga ayyukan zamanintar da kasar Sin. Kaza lika, kasar Sin za ta kara kyautata ayyukan raya zaman al’umma, da daidaita batutuwa manya da kanana na al’umma, ta yadda kowa zai kara farin ciki da walwala.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Shugaba Xi ya ce, yayin da ake gaggauta samun manyan sauye-sauyen yanayin da ake ciki a duniya, kamata ya yi sassan kasa da kasa su kai zuciya nesa, su mai da hankali a kan makomar dan Adam. Kasar Sin na son yin kokari tare da sassan kasa da kasa, wajen zama masu hadin gwiwar sada zumunta da juna, masu sa kaimin musayar wayewar kai, kuma masu gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya ga dukkanin bil Adam, don samar da kyakkyawar makomar duniya. (Murtala Zhang&Lubabatu Lei)

Xi Jinping
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Xi Jinping
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Kwamitin Kasa Na Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ya Yi Bikin Maraba Da Sabuwar Shekara

Kwamitin Kasa Na Majalisar CPPCC Ta Kasar Sin Ya Yi Bikin Maraba Da Sabuwar Shekara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.