• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Ya Aike Da Wasikar Taya Murnar Bude Dandalin Sada Zumunta Tsakanin Al’ummun Sin Da Amurka

by CMG Hausa
2 years ago
Shugaban kasar Sin

A yau Laraba ne shugaban kasar Xi Jinping, ya aike da sakon taya murnar bude dandalin sada zumunta tsakanin al’ummun Sin da na Amurka da ke da taken “Alaka da Kuliang”, inda a cikin sakon na sa ya jaddada cewa, tushen ci gaban alakar sassan biyu ya ta’allaka ne kan hadin kan al’ummunsu. 

Kaza lika shugaba Xi ya yi fatan cewa, dukkanin al’ummun sassan biyu za su yayata labarin “Kuliang”, tare da ingiza ma’anar sa, ta yadda zumuntar dake tsakanin Sin da Amurka zai ci gaba da wanzuwa yadda ya kamata.

  • Firaministan Kasar Sin Ya Jaddada Hadin Kai Da Hadin Gwiwa A Taron Davos

A shekarar 1901, iyayen wani jariri Ba’Amurke mai suna Milton Gardner, sun zo da shi birnin Fuzhou na kasar Sin. Kuma a shekarar 1911, shi da iyalansa suka koma Amurka. To sai dai bayan hakan mista Gardner ya ci gaba da kaunar sake komawa garin sa dake kasar Sin, amma bai samu zarafin yin hakan ba har ya rasu.

Da taimakon wasu daliban kasar Sin da ke dalibta a Amurka, uwar gidan Gardner ta gano garin da marigayi mijin ta ke fatan ziyarta a kasar Sin shi ne Kuliang dake Fuzhou.

A shekarar 1992, shugaba Xi Jinping, wanda a lokacin shi ne sakataren kwamitin JKS reshen birnin Fuzhou, ya samu wannan labari mai taba zuciya game da Kuliang, don haka ya gayyaci uwar gidan Gardner da ta ziyarci kasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

A shekarar 2012, lokacin da Xi Jinping ke matsayin mataimakin shugaban kasar Sin, ya ziyarci Amurka, inda ya ba da labarin Kuliang yayin liyafar da kawayen Sin dake Amurka suka shirya, labarin da ya yi matukar jan hankali al’ummu masu yawa daga sassan kasashen 2.

Dandalin sada zumunta tsakanin al’ummun Sin da Amurka ya gudana a birnin Fuzhou fadar mulkin lardin Fujian a yau Larabaa. (Saminu Alhassan)

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Next Post
Bikin Babbar Sallah: Tinubu Zai Sake Inganta Ababen More Rayuwa – Shettima

Bikin Babbar Sallah: Tinubu Zai Sake Inganta Ababen More Rayuwa - Shettima

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.