• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Tattalin Arzikin Duniya Na St. Petersburg

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Tattalin Arzikin Duniya Na St. Petersburg

新华社照片,北京,2022年6月17日 习近平出席第二十五届圣彼得堡国际经济论坛全会并致辞 6月17日晚,国家主席习近平应邀以视频方式出席第二十五届圣彼得堡国际经济论坛全会并致辞。 新华社记者 鞠鹏 摄

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya halarta tare da gabatar da jawabi ga taron tattalin arzikin duniya karo na 25 da aka yi a St. Petersburg.

Xi Jinping, wanda ya halarci taron ta kafar bidiyo bisa gayyatar da aka yi, ya ce duniya na fuskantar muhimman sauye-sauye da annoba da ba a taba gani ba cikin karni, kana dunkulewar tattalin arzikin duniya ya gamu da tsaiko, baya ga kalubalen da ake fuskanta wajen aiwatar da muradun ci gaba masu dorewa da MDD ke son cimmawa zuwa shekarar 2030.

Ya ce a lokacin da duniya ke da burin samun ci gaba mai dorewa cikin daidaito, ya kamata a yi amfani da damarmakin dake akwai wajen tunkarar kalubalen da ake fuskanta da hada hannu wajen aiwatar da shirin ci gaban duniya domin gina al’umma mai kyakkyawar makoma da zaman lafiya.
Ya kara da cewa, da farko, akwai bukatar samar da kyakkyawan yanayin neman ci gaba. Na biyu, ya kamata a karfafa hadin gwiwa a fannin neman ci gaba. Na uku, a inganta dunkulewar tattalin arzikin duniya, sai na hudu, a ingiza neman ci gaba ta hanyar kirkire-kirkire.

Bugu da kari, shugaban na Sin ya ce tubalin tattalin arzikin kasarsa na juriya da karfi kuma mai dorewa cikin lokaci mai tsawo, bai sauya ba. kuma ana da kwarin gwiwa kan bunkasar tattalin arzikin kasar.

Har ila yau, shugaban na kasar Sin ya ce Sin za ta ci gaba da neman ci gaba mai inganci da fadada manufar bude kofa ga ketare da ingiza hadin gwiwa mai inganci kan shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya”. (Fa’iza Mustapha)

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

 

 

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

ISWAP Ta Sace Ma’aikatan Agaji 3, Ta Kashe Jami’an Tsaro 3 A Borno

Next Post

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Sauya Kwalejin Ilimi Ta Bichi Zuwa Jami’ar Kimiya Da Fasaha

Related

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli
Daga Birnin Sin

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

17 hours ago
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

19 hours ago
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13
Daga Birnin Sin

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

20 hours ago
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka
Daga Birnin Sin

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

20 hours ago
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya
Daga Birnin Sin

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

21 hours ago
Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya

23 hours ago
Next Post
Majalisar Dattawa Ta Amince Da Sauya Kwalejin Ilimi Ta Bichi Zuwa Jami’ar Kimiya Da Fasaha

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Sauya Kwalejin Ilimi Ta Bichi Zuwa Jami'ar Kimiya Da Fasaha

LABARAI MASU NASABA

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA

July 4, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

July 4, 2025

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

July 4, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

July 4, 2025
Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

Ba A Taɓa Nuno Bidiyon Shugaban Jam’iyyarmu Ta ADC Yana Cusa Dala A Aljihu Ba —Dalung

July 4, 2025
Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (1)

July 4, 2025
Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci

July 4, 2025
Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace

July 4, 2025
‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

‘Yan Nijeriya Na Kewar Buhari Saboda Azabar Da Suke Fuskanta A Hannun Tinubu – Amaechi

July 4, 2025
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Kungiyar MEMAN Ta Yi Maraba Da Shirin Dangote Na Rabar Da Man Fetur

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.