• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Shugabannin Kasashen Faransa Da Jamus Da Argentina A Gefen Taron Kolin G20

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Shugabannin Kasashen Faransa Da Jamus Da Argentina A Gefen Taron Kolin G20
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron, da shugaban gwamnatin kasar Jamus Olaf Scholz, da kuma shugaban kasar Argentina Javier Milei a gefen taron kolin kungiyar G20 a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil. 

 

Yayin ganawarsa da shugaban kasar Faransa, Xi ya ce, Sin da Faransa manyan kasashe ne dake da cikakken ‘yancin kai dake sauke nauyin dake wuyansu, huldarsu na da babbar daraja a bangaren manyan tsare-tsare da babbar ma’ana a duk fadin duniya. Ya kamata, bangarorin biyu su zurfafa cudanya ta fuskar manyan tsare-tsare da kara goyawa juna baya, ta yadda za a tabbatar da bunkasuwar huldar kasashen biyu mai dorewa da yakini, don taka rawar gani kan raya huldar Sin da Turai yadda ya kamata da zaman lafiya da kwanciyar hankalin duniya.

  • Pep Guardiola Ya Tsawaita Kwantiragi A Manchester City Har Zuwa Shekarar 2027
  • Sin Tana Fatan Raya Duniya Mai Adalci Dake Samun Bunkasuwa Tare Tsakanin Mabambantan Bangarori

Haka kuma, a yayin ganawarsa da shugaban gwamnatin kasar Jamus, Xi Jinping ya bayyana cewa, akwai bukatar kasashen Sin da Jamus su duba da raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu na dogon lokaci bisa manyan tsare-tsare. Ya bayyana cewa, bangarorin biyu sun yi tattaunawa ta gaskiya, mai zurfi da kyakkyawar sakamako yayin ziyarar da Scholz ya kawo kasar Sin a watan Afrilu. Yana mai cewa, a cikin watannin da suka gabata, hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu ya samu sakamako mai ma’ana a fannonin samun bunkasuwa ba tare da gurbata muhalli ba, da sufuri mai dorewa, da hadin gwiwar raya aikin gona a Afirka, yayin da dangantakar dake tsakanin kasashen biyu ke ci gaba da nuna sabon karfi da kuzari.

 

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Bugu da kari, a yayin ganawarsa da shugaban kasar Argentina, Kasashen Sin da Argentina sun yi alkawarin ba da goyon baya wajen inganta raya shawarar “Ziri daya da hanya daya”. Da yake karin haske game da makomar hadin gwiwar da za a yi gaba, Xi ya ce, tsarin tattalin arziki da cinikayya na kasashen Sin da Argentina sun yi matukar dacewa da juna, yana mai bayyana fatan bangarorin biyu za su iya fadada hadin gwiwa a fannonin makamashi, da samar da ababen more rayuwa na ma’adinai, da aikin gona, da kimiyya da fasaha, da tattalin arziki na dijital. (Mai Fassara: Amina Xu, Mohammed Baba Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kama Dillalin Safarar Makamai Dan Aljeria A Zamfara 

Next Post

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Babban Taron Intanet Na Duniya Na Bana A Wuzhen

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

14 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

15 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

17 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

20 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

21 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

22 hours ago
Next Post
Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Babban Taron Intanet Na Duniya Na Bana A Wuzhen

Xi Ya Mika Sakon Taya Murna Ga Babban Taron Intanet Na Duniya Na Bana A Wuzhen

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.