• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Karin Girma Ga Jami’ai 4,526

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Shugaban NIS Isah Jere Ya Sanar Da Karin Girma Ga Jami’ai 4,526
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta kasa, Isah Jere Idris ya sanar da karin girma ga jami’an hukumar su 4,526 da suka yi jarrabawar karin girma da wadanda suka samu horaswa daban-daban ta daga darajar mukami a shekarar 2021.

Tabbatar da karin girman na kunshe ne a cikin wasikar da ta zo daga Hukumar Gudanarwar Rundunonin da ke karkashin Ma’aikatar Cikin Gida da aka yi wa lambar CDCFIB/S.33/BOLIII/54 mai dauke da kwanan wata,18 ga Agusta, 2022.

  • Malam Yaya Siffar Wankan Janaba Take?
  • Jami’an Kashe Gobara Sun Ceto Mutum 91 Da Dukiyar Da Ta Kai Kusan Naira Miliyan 25 A Kano

Shugaban hukumar ya bayyana hakan ne a yau a hedikwatarta yayin da yake yi wa wasu jami’ai masu taimaka masa da ke cikin ma’aikatan da aka yi wa karin girma ado da sabbin mukamansu.

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulda da jama’a na NIS, wanda shi ma aka kara masa girma daga karamin Mataimakin Kwanturola (ACI) zuwa Babban Mataimakin kwanturola (DCI), Amos Okpu, ta ce jami’ai masu mukamin karamin mataimakan Kwanturola 145 sun samu karin girma zuwa Babban Mataimakin Kwanturolan Shige da Fice; sannan masu mukamin Babban Sufiritanda 99 sun samu karin girma zuwa karamin mataimakin Kwanturola.

Bugu da kari, akwai masu mukamin Sufiritanda 307 da aka mayar da su matsayin Babban Sufiritanda; kana mataimakan Sufiritanda 338 sun samu ci gaba zuwa matsayin Sufiritanda.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Sauran wadanda suka samu karin girman su ne jami’ai 589 da aka ciyar da su gaba zuwa mukamin mataimakin Sufiritanda na daya (I), sai wasu 794 da aka kara musu mukami zuwa Mataimakan Sufiritanda na biyu (II).
Har ila yau takardar ta yi bayanin cewa, jami’ai masu mukamin Sufeto 21 sun samu ci gaba zuwa mataimakin Sufiritanda na biyu (II).

Yayin da wasu jami’ai 1254 suka sami ci gaba zuwa matsayi na Mataimakin Sufeto na biyu (II), kana akwai jimillar kananan jami’ai 979 da suka samu kwarewar aiki da aka daga darajarsu zuwa matsayi na Mataimakin Sufiritanda na biyu.

Da yake jawabi a wajen bikin adonta mukarrabansa, Shugaban NIS CGI Isah Jere Idris ya yaba wa Ministan Harkokin Cikin Gida, Ogbeni Rauf Aregbesola wanda kuma ya zama shugaban hukumar gudanarwar rundunonin da ke karkashin ma’aikatar bisa jajircewarsa wajen ciyar da ma’aikata gaba.

Ya bukaci sabbin jami’an da aka kara musu girma da su kara kwazo da saka karamcin da aka yi musu ta hanyar sadaukarwa da kuma biyayya a bakin aiki.

Ya kuma bai wa gwamnati tabbacin cewa hukumar a karkashinsa za ta ci gaba da bayar da gudunmawa mai amfani ga zaman lafiya da ci gaban kasa.

Daga cikin jami’an da aka yi wa ado da sabbin mukamansu akwai Jami’in hulda da jama’a na NIS Amos OKPU, wanda aka kara wa girma zuwa DCI; da Jami’in kula da tsare-tsare na Kwanturola Janar MY Dutse mai barin gado da magajinsa MA Ajimobi wanda a yanzu suka zama Manyan Mataimakan Kwanturola.

Sauran sun hada da Mercy Gadzama, Manajar Kula da Cibiyar Fasaha ta NIS, da a yanzu ta zama Babbar Sufiritanda, da Jami’in Tsaro na Kwanturola Janar AO Olukoya, da aka kara masa girma zuwa mukamin Babban Sufiritanda da Tanko Godiya da Nguar Loice Titus na Sashen Kai daukin Gaggawa (RRS), duka biyu da aka kara musu girma zuwa mataimakan Sufiritanda na Shige da Fice (II).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jami'aiJereKarin GirmaNIS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abin Da Ya Sa Mata Suka Fi Fuskantar Yiwuwar Kashe Kansu —Farfesa Aishatu

Next Post

Dattijo Mai Shekara 74 Ya Yi Aurensa Na Farko A Lakwaja

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

25 minutes ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

3 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

17 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

17 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

18 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

19 hours ago
Next Post
Dattijo Mai Shekara 74 Ya Yi Aurensa Na Farko A Lakwaja

Dattijo Mai Shekara 74 Ya Yi Aurensa Na Farko A Lakwaja

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.