ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban PDP Na Shiyyar Kudu Maso Yamma, Adagunodo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 62

by Sadiq
3 years ago
PDP

Shugaban jam’iyyar PDP na shiyyar Kudu maso Yamma, Hon. Soji Adagunodo, ya rasu.

Da yake sanar da rasuwar Hon. Adagunodo a wani sako da aka saki a ranar Talata da safe, dansa, Oluwatukesi Adagunodo, ya ce mahaifinsa ya rasu yana da shekaru 62.

  • FAAN Ta Bai Wa Kamfanonin Jirage Umarnin Kwashe Jiragensu Daga Filin Jirgin Saman Abuja
  • Wani Babban Dalilin Da Ya Haifar Da Hargitsi A Kasar Sudan

Adagunodo wanda tsohon shugaban jam’iyyar ne a Jihar Osun, ya kuma taba zama dan majalisa a majalisar dokokin jihar wanda ya wakilci mazabar jihar Obokun.

ADVERTISEMENT

Sai dai ba a gano musabbabin mutuwarsa ba kamar yadda ya zuwa lokacin hada wannan rahoto, an ce ya rasu ne bayan gajeriyar rashin lafiya.

Majiyar iyalinsa sun tabbatar da rasuwarsa a Amurka.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

A cikin sakon ta’aziyyarsa mai dauke da sa hannun mai magana da yawunsa, Mallam Olawale Rasheed, Gwamna Ademola Adeleke na Jihar Osun, ya bayyana kaduwarsa da labarin rasuwar shugaban jam’iyyar, inda ya bayyana rasuwarsa a matsayin “rashi mai zafi ba ga jam’iyyar kadai ba, har da Jihar Osun.”

Gwamna Adeleke ya bayyana rashin Hon. Adagunodo ya bayyana gudunmawar da ya bayar ga PDP ga ayyukan da ya yi daban-daban.

“Marigayi Hon. Adagunodo abokina ne da na goyi bayan ya zama Shugaban jam’iyyar PDP na Jiha wanda kuma shi ne ya bani goyon bayan na zama Sanatan Tarayya, babban rashi ne kuma za mu yi kewarsa matuka.

“Labarin rasuwar Honarabul Adagunodo ya yi matukar bata min rai a matsayina na mutum, ina lura da irin gudunmawar da Adagunodo ya bai wa babbar jam’iyyarmu a matsayinsa na shugaban jam’iyyar a Jihar Osun kuma ina murnar irin tasirin da ya yi a matsayinsa na Shugaban PDP na Kudu maso Yamma.

“Ina cikin bakin cikin rashinsa, ina tunawa da kyakkyawar mu’amala da muka yi tare.

“Addu’armu Allah Madaukakin Sarki Ya jikansa ya kuma sa Adagunodo ya huta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86
Da ɗumi-ɗuminsa

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta
Da ɗumi-ɗuminsa

ASUU Ta Dakatar Da Yajin Aiki, Ta Bai Wa Gwamnati Wa’adin Wata Guda Don Biyan Buƙatunta

October 22, 2025
Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas
Da ɗumi-ɗuminsa

Gobara Ta Tashi A Kasuwar Alaba Da Ke Legas

October 22, 2025
Next Post
An Kashe Mutum 16 A Rikicin ‘Yan Kungiyar Asiri A Akwa Ibom

An Kashe Mutum 16 A Rikicin ‘Yan Kungiyar Asiri A Akwa Ibom

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025
Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

Madalla Da Sabon Binciken Jami’ar Nankai Ta Kasar Sin Kan Mata Marasa Haihuwa

November 12, 2025
'yansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutane 4 Kan Zargin Fashi Da Makami A Bauchi

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.