• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wani Babban Dalilin Da Ya Haifar Da Hargitsi A Kasar Sudan

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Wani Babban Dalilin Da Ya Haifar Da Hargitsi A Kasar Sudan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanin kowa ne, kasar Amurka tana kallon kanta a matsayin “mai kare tsarin Demokuradiyya” a duniya. Sai dai yunkurin kasar na “kare Demokuradiyya” ya kan haddasa ta’asa a sauran kasashe.

Kwanan baya, na karanta wani bayanin da shafin yanar gizo na jaridar New York Times ta kasar Amurka ya watsa, mai taken “ Yadda yunkurin kasar Amurka na tabbatar da tsarin Demokuradiyya a Sudan ya haddasa yaki a kasar”.

  • Karuwar Cinikin Wajen Sin A Watanni 4 Na Farkon Bana Ta Kai Kaso 5.8 Bisa Dari Kan Na Makamancin Lokaci Na Bara

Marubucin wannan bayani ya ce, kasar Amurka ta dade tana kokarin mai da kasar Sudan wani misali na gwajin yada tsarin Demokuradiyya a sauran kasashe, inda ta yi ta shisshigi cikin harkokin siyasa na kasar. Sai dai kamar yadda ake cewa “Domin auki ake yin kunu ya komo ya rasa auki”, goyon bayan da kasar Amurka ta nuna wa manyan hafsoshin kasar Sudan ya sa su girman kai da kwadayin ikon mulki, lamarin da ya sa ake samun barkewar wutar yaki a kasar yanzu.

Wannan bayani ya nuna yadda kafofin watsa labaru na kasar Amurka suka yi tsokaci game da manufar kasar ta “yada tsarin Demokuradiyya” a duniya. Ra’ayin marubucin bayanin na “manufar kasar Amurka ta haddasa hargitsi a kasar Sudan” ya yi daidai, amma bai fayyace ainihin dalilin da ya sa ake samun wannan sakamako ba.

A ganinsa, idan kasar Amurka ta saka wa shugabannin sojojin kasar Sudan takunkumi a maimakon nuna musu goyon baya, to, za a iya tabbatar da tsarin Demokuradiyya a kasar. Sai dai, a hakika, yadda kasar Amurka take shisshigi a harkokin kasar Sudan, da fakewa da batun Demokuradiyya, shi ne babban dalilin da ya sa ake ta samun rikice-rikice a kasar.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Tun da tsohon shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir ya kama mulki a shekarar 1989, kasar Amurka ta fara kokarin neman kawo karshen mulkinsa. Daga farkon shekarun 1990, kasar Amurka ta hure wa gamayyar kasa da kasa kunne, don su dakatar da samar da tallafi da rance ga kasar Sudan, bisa dalilin wai kasar na “keta hakkin dan Adam”.

Daga baya, kasar Amurka ta kara sanya wa kasar Sudan takunkumi, bisa zarginta da “nuna goyon baya ga ‘yan ta’adda”. Matakan da kasar Amurka ta dauka sun sa Sudan zama wata kasa dake “rike da kwanon zinariya tana barace-barace”, ganin yadda kasar ta kasa raya tattalin arzikinta, inda ta kai har kashi 47% na al’ummar kasar sun tsunduma cikin tsananin talauci, duk da kasar na mallakar dimbin albarkatun kasa, ciki har da danyen mai.

Ban da matakan tattalin arziki, kasar Amurka ta kuma dauki matakai na siyasa, don neman hambarar da shugaba al-Bashir. Inda ta dade tana samar da tallafi ga dakaru masu adawa da gwamnatin Sudan, ciki har da dakarun yankin Darfur, da na yankin da aka fi samun danyen mai dake kudancin kasar. Lamarin da ya sa ake ta samun tashin hankali a kasar Sudan, da yukurin ballewar yankin kudancin kasar, wanda ya zama kasar Sudan ta Kudu daga bisani.

Wannan lamari ya sa kasar Sudan asarar kashi 70% na albarkatun mai, da fuskantar raguwar kudin shiga, da tsanantar yanayin koma bayan tattalin arziki, abun da ya sa dimbin jama’ar kasar aiwatar da zanga-zanga a wurare daban daban sakamakon matukar fushi. Daga baya, bisa goyon bayan da kasar Amurka ta bayar, Abdel Fattah al-Burhan, da sauran manyan hafsoshin rundunar sojan kasar suka kaddamar da juyin juya hali, wanda ya kai ga hambarar da shugaba Omar al-Bashir a shekarar 2019.

Kasar Amurka ta kwashe shekaru 30 tana kokarin neman kawo karshen mulkin Omar al-Bashir, kuma a karshe ta samu biyan bukata. Sai dai hakan bai sa kasar Sudan karkata ga turbar Demokuradiyya ba.

Maimakon haka, an dade ana samun ja-in-ja tsakanin rukunonin sojan kasar. Har ma wannan yanayi ya sa an sa kafar wando daya, tare da juyewa zuwa wani babban tashin hankali mai tsanani yanzu. Sai dai sau da yawa mun ga abkuwar makamancin hakan, inda kasar Amurka ta yi shisshigi cikin harkokin gidan sauran kasashe, har ma ta hambarar da gwamnatocin kasashen, ta fakewa da “kare Demokuradiyya”, daga baya kuma kasashen suka fada cikin tarkon tashin hankali, da tabarbarewar tattalin arziki. Kuma da wuya su iya fitar da kansu daga cikin irin wannan tarko. Wannan lamari ya taba faruwa a kasashen Iraki, da Afghanistan, da kuma Libya.

Bayanin jaridar New York Times ya nuna cewa, ko Amurkawa ma ba su gamsu da matakan gwamnatin kasarsu na yada tsarin Demokuradiyya ba. A ganinsu, watakila za a iya daidaita aikin, ta hanyar kyautata dabarun shisshigi, misali nuna goyon baya, ko kuma sanya takunkumi kan sauran mutane.

Duk da haka, a matsayin mu na mutane na sauran kasashe, abin da muke son fada shi ne: Lokaci ya yi a kawo karshen girman kai na kasar Amurka. Idan kasar za ta iya girmama ikon mulkin kai na sauran kasashe, da daina yin shisshigi cikin harkokin gidansu, to, hakan zai iya zama gudunmowa mafi girma da kasar Amurka za a iya samar wa duniya, a fannin kare darajar Demokuradiyya. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasashen Gabas Ta Tsakiya Sun Sake Bayyana Adawa Da Yunkurin Amurka

Next Post

FAAN Ta Bai Wa Kamfanonin Jirage Umarnin Kwashe Jiragensu Daga Filin Jirgin Saman Abuja

Related

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

10 hours ago
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

11 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

13 hours ago
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

14 hours ago
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

15 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

16 hours ago
Next Post
FAAN Ta Bai Wa Kamfanonin Jirage Umarnin Kwashe Jiragensu Daga Filin Jirgin Saman Abuja

FAAN Ta Bai Wa Kamfanonin Jirage Umarnin Kwashe Jiragensu Daga Filin Jirgin Saman Abuja

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.