• English
  • Business News
Friday, September 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

by Sulaiman
3 weeks ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Uganda Yoweri Museveni, ya ce jarin kasar Sin na taimakawa wajen gaggauta ci gaban nahiyar Afirka, musamman ta fuskar samar da ababen more rayuwa da raya masana’antu.

Shugaba Museveni, wanda ya bayyana hakan a jiya Litinin, yayin bude taron hada-hadar kudaden samar da ci gaba na kasar Uganda na shekarar nan ta 2025, ya ce kamfanonin Sin masu zaman kansu da na gwamnati, sun taka rawar gani wajen samar da hanyoyin sufuri, da ayyukan bunkasa makamashi, ayyukan da ya bayyana a matsayin ginshikan bude kofofin raya nahiyar Afirka.

An dai kaddamar da taron na yini biyu ne a birnin Kampala fadar mulkin kasar Uganda, bisa taken “Sauya akalar Afirka ta hanyar bunkasa tsarin samar da kudade”. Taron ya kuma yi bitar irin rawar da masu zuba jari na kasar Sin suka taka wajen kafa yankunan masana’antu a sassan Afirka.

A cewar shugaba Museveni, irin wadannan yankunan masana’antu, baya ga tallafawa da suke yi wajen rage kashe kudaden shigo da hajoji, suna kuma samar da dubban guraben ayyukan yi ga matasan kasashen nahiyar.

Ya ce “Sabanin jagororin kasashen yamma, kasar Sin ta yi amfani da tarin damammakin da ta samu a Afirka, wajen zuba jari tare da alkawarta samar da gajiya mai dumbin yawa, don haka ya yi kira ga masu samar da lamuni na yammacin duniya da su dauki darasi daga kasar Sin, ta hanyar fadada samar da basussuka masu sauki ga kasashen Afirka, maimakon barin masu bayar da lamuni masu zaman kansu, suna sanya kudin ruwa mai tarin yawa kan lamunin da suke baiwa kasashen na Afirka. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

Next Post

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Related

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

15 hours ago
Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

16 hours ago
Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya
Daga Birnin Sin

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

18 hours ago
An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York

18 hours ago
Xi Ya Sanar Da Gudummawar Kasarsa Dangane Da Tunkarar Sauyin Yanayi Nan Zuwa 2035
Daga Birnin Sin

Xi Ya Sanar Da Gudummawar Kasarsa Dangane Da Tunkarar Sauyin Yanayi Nan Zuwa 2035

1 day ago
Sin Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kai
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kai

1 day ago
Next Post
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

Goron Sallah

GORON JUMA’A

September 26, 2025
NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

NECO 2025: Gwamnan Kano Ya Bayyana Bayanai Ba Daidai Ba

September 26, 2025
Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar

Yadda Sauye-Sauyen Da Aka Yi A Fannin Mai Da Iskar Gas Suka Samar Da Gagarumin Ci Gaba A Wannan Shekarar

September 26, 2025
Manyan Ƴan Siyasa Sun Yi Watsi Da Kafa Sabuwar Jam’iyyar ADA Sun Rungumi ADC

Manyan Ƴan Siyasa Sun Yi Watsi Da Kafa Sabuwar Jam’iyyar ADA Sun Rungumi ADC

September 26, 2025
Manyan Motoci 2,000 A Kullum Ke Zirga-zirga A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas —Rahoto

Manyan Motoci 2,000 A Kullum Ke Zirga-zirga A Tashoshin Jiragen Ruwa Na Jihar Legas —Rahoto

September 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Mika Ƙorafe-Ƙorafe Kan Sheikh Lawan Triumph Zuwa Majalisar Shura

Gwamnatin Kano Ta Mika Ƙorafe-Ƙorafe Kan Sheikh Lawan Triumph Zuwa Majalisar Shura

September 26, 2025
‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

‘Yancin Kananan Hukumomi: Yadda Gwamnoni Suke Kawo Cikas

September 26, 2025
Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

Kwankwaso na Tattaunawa da Shugaban APC Nentawe A Shirye-shiryen Sauya Sheƙa

September 26, 2025
Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

Yadda Aka Gudanar Da Taron Tuna Shekara 20 Da Rasuwar Dr Bala Usman

September 26, 2025
Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya

Ya Kamata Karancin Malamai A Duniya Ya Zama Darasi Ga Nijeriya

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.