ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugaban Uganda: Jarin Sin Na Taimakawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Kasashen Afirka

by Sulaiman
10 months ago
Uganda

Shugaban kasar Uganda Yoweri Museveni, ya ce jarin kasar Sin na taimakawa wajen gaggauta ci gaban nahiyar Afirka, musamman ta fuskar samar da ababen more rayuwa da raya masana’antu.

Shugaba Museveni, wanda ya bayyana hakan a jiya Litinin, yayin bude taron hada-hadar kudaden samar da ci gaba na kasar Uganda na shekarar nan ta 2025, ya ce kamfanonin Sin masu zaman kansu da na gwamnati, sun taka rawar gani wajen samar da hanyoyin sufuri, da ayyukan bunkasa makamashi, ayyukan da ya bayyana a matsayin ginshikan bude kofofin raya nahiyar Afirka.

An dai kaddamar da taron na yini biyu ne a birnin Kampala fadar mulkin kasar Uganda, bisa taken “Sauya akalar Afirka ta hanyar bunkasa tsarin samar da kudade”. Taron ya kuma yi bitar irin rawar da masu zuba jari na kasar Sin suka taka wajen kafa yankunan masana’antu a sassan Afirka.

ADVERTISEMENT

A cewar shugaba Museveni, irin wadannan yankunan masana’antu, baya ga tallafawa da suke yi wajen rage kashe kudaden shigo da hajoji, suna kuma samar da dubban guraben ayyukan yi ga matasan kasashen nahiyar.

Ya ce “Sabanin jagororin kasashen yamma, kasar Sin ta yi amfani da tarin damammakin da ta samu a Afirka, wajen zuba jari tare da alkawarta samar da gajiya mai dumbin yawa, don haka ya yi kira ga masu samar da lamuni na yammacin duniya da su dauki darasi daga kasar Sin, ta hanyar fadada samar da basussuka masu sauki ga kasashen Afirka, maimakon barin masu bayar da lamuni masu zaman kansu, suna sanya kudin ruwa mai tarin yawa kan lamunin da suke baiwa kasashen na Afirka. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Uganda
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa
  • Sulaiman
    An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara
  • Sulaiman
    2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara
  • Sulaiman
    Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

MASU ALAKA

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa
Daga Birnin Sin

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce
Daga Birnin Sin

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Next Post
Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

Babban Sakataren MDD: Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026
Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

July 12, 2026
Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

July 12, 2026
‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026
An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

July 12, 2026
NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli

July 12, 2026
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

July 12, 2026
NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.