• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin Nijeriya: ‘Yan Arewa Ku Jira Har Zuwa 2031 —Sakataren Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Labarai
0
Shugabancin Nijeriya: ‘Yan Arewa Ku Jira Har Zuwa 2031 —Sakataren Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya bukaci jiga-jigan siyasar Arewa masu yunkurin tsayawa takarar shugabancin kasa a 2027 da su kawar da burinsu su jira har zuwa 2031 lokacin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kammala wa’adinsa na biyu.

Akume dai ya bukaci tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da ya halakar da tunaninsa na karbar mulki a shekarar 2027, inda ya ce idan Allah ya nufa zai zama shugaban, to zai iya lashe zabe ne kawai yana da shekaru 90 a duniya.

  • Dattawan Arewa Sun Dukufa Wajen Warware Rikicin Siyasar Da Ta Kunno Kai A Kungiyar ACF
  • Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya Tare Da Ƙona Gidaje A Gombe

Akume, wanda ya yi magana a ranar Lahadin da ta gabata yayin wani shiri na TBC kan harkokin siyasa, ya ce har yanzu lokaci ne na Kudu wajen samar da shugaban kasa a 2027.

Sakataren gwamnatin tarayya wanda tsohon gwamnan Jihar Benuwai ne, ya ce Shugaba Tinubu bai rasa goyon bayan ‘yan Nijeriya ba, sakamakon kudirin gyara dokar haraji da sauran tsare-tsarensa na tattalin arziki da aka dauka a cikin watanni 17 na gwamnatinsa, ya kuma bayyana fatansa na cewa Tinubu zai jagoranci Nijeriya har na tsowon shekaru 8.

Ya kare kudirin sake fasalin haraji a matsayin wasu tsare-tsare masu kyau da za su taimaki kasar nan idan har majalisar dokoki ta amince da su.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Ya ce, “Ya kamata a bar Shugaba Tinubu a matsayinsa na dan Kudu ya sake yin wa’adi na biyu, ma’ana wadanda ke sa ido a kan smun shugabanci daga Arewa a 2027 su jira har 2031.

“Idan har Allah ya nufa Alhaji Atiku Abubakar zai zama shugaban Nijeriya, ko da yana da shekara 90, zai iya samun haka. Amma shi da sauran ’yan Arewa da ke sa ido kan ofishin shugaban kasa a 2027 su jira har Tinubu ya kammala wa’adinsa karo na biyu.”

Akume ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su kyale kudirin dokar sake fasalin haraji su daidaita ta hanyoyin da ake bukata na majalisa, yana mai cewa, “Suna da kyakkyawar manufa ga Nijeriya da ‘yan Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwamitin Amintattun PDP Ya Dage Kan Mika Shugabancin Jam’iyyar Ga Sashin Arewa Ta Tsakiya

Next Post

Hukumar NPA Ta Ƙara  Kaimi Wajen Janyo Masu Zuba Hannun Jari

Related

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
Labarai

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

45 minutes ago
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Manyan Labarai

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

3 hours ago
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

4 hours ago
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

13 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

14 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

15 hours ago
Next Post
Hukumar NPA Ta Ƙara  Kaimi Wajen Janyo Masu Zuba Hannun Jari

Hukumar NPA Ta Ƙara  Kaimi Wajen Janyo Masu Zuba Hannun Jari

LABARAI MASU NASABA

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.