• English
  • Business News
Friday, May 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin Nijeriya: ‘Yan Arewa Ku Jira Har Zuwa 2031 —Sakataren Gwamnatin Tarayya

by Yusuf Shuaibu
5 months ago
in Labarai
0
Shugabancin Nijeriya: ‘Yan Arewa Ku Jira Har Zuwa 2031 —Sakataren Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakataren Gwamnatin Tarayya, Sanata George Akume, ya bukaci jiga-jigan siyasar Arewa masu yunkurin tsayawa takarar shugabancin kasa a 2027 da su kawar da burinsu su jira har zuwa 2031 lokacin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kammala wa’adinsa na biyu.

Akume dai ya bukaci tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da ya halakar da tunaninsa na karbar mulki a shekarar 2027, inda ya ce idan Allah ya nufa zai zama shugaban, to zai iya lashe zabe ne kawai yana da shekaru 90 a duniya.

  • Dattawan Arewa Sun Dukufa Wajen Warware Rikicin Siyasar Da Ta Kunno Kai A Kungiyar ACF
  • Yan Bindiga Sun Kashe Mutum Ɗaya Tare Da Ƙona Gidaje A Gombe

Akume, wanda ya yi magana a ranar Lahadin da ta gabata yayin wani shiri na TBC kan harkokin siyasa, ya ce har yanzu lokaci ne na Kudu wajen samar da shugaban kasa a 2027.

Sakataren gwamnatin tarayya wanda tsohon gwamnan Jihar Benuwai ne, ya ce Shugaba Tinubu bai rasa goyon bayan ‘yan Nijeriya ba, sakamakon kudirin gyara dokar haraji da sauran tsare-tsarensa na tattalin arziki da aka dauka a cikin watanni 17 na gwamnatinsa, ya kuma bayyana fatansa na cewa Tinubu zai jagoranci Nijeriya har na tsowon shekaru 8.

Ya kare kudirin sake fasalin haraji a matsayin wasu tsare-tsare masu kyau da za su taimaki kasar nan idan har majalisar dokoki ta amince da su.

Labarai Masu Nasaba

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Ya ce, “Ya kamata a bar Shugaba Tinubu a matsayinsa na dan Kudu ya sake yin wa’adi na biyu, ma’ana wadanda ke sa ido a kan smun shugabanci daga Arewa a 2027 su jira har 2031.

“Idan har Allah ya nufa Alhaji Atiku Abubakar zai zama shugaban Nijeriya, ko da yana da shekara 90, zai iya samun haka. Amma shi da sauran ’yan Arewa da ke sa ido kan ofishin shugaban kasa a 2027 su jira har Tinubu ya kammala wa’adinsa karo na biyu.”

Akume ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su kyale kudirin dokar sake fasalin haraji su daidaita ta hanyoyin da ake bukata na majalisa, yana mai cewa, “Suna da kyakkyawar manufa ga Nijeriya da ‘yan Nijeriya.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwamitin Amintattun PDP Ya Dage Kan Mika Shugabancin Jam’iyyar Ga Sashin Arewa Ta Tsakiya

Next Post

Hukumar NPA Ta Ƙara  Kaimi Wajen Janyo Masu Zuba Hannun Jari

Related

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?
Ra'ayi Riga

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

57 minutes ago
Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

2 hours ago
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum
Labarai

‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Na’urorin Zamani Daidai Lokacin Da Sojoji Ke Da Karancin Makamai -Zulum

3 hours ago
Dan Asalin Jihar Kano Ya Kafa Tarihin Kirkirar Manhaja Mai Auna Tsayin Bishiya A Faransa
Labarai

Dan Asalin Jihar Kano Ya Kafa Tarihin Kirkirar Manhaja Mai Auna Tsayin Bishiya A Faransa

4 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jaridar Da Ya Fallasa ‘Sharrin’ Da Ake Shirya Wa Natasha
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jaridar Da Ya Fallasa ‘Sharrin’ Da Ake Shirya Wa Natasha

4 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Labarai

Tinubu Ya Amince Da Lasisin Aikin Hakar Mai A Arewa

5 hours ago
Next Post
Hukumar NPA Ta Ƙara  Kaimi Wajen Janyo Masu Zuba Hannun Jari

Hukumar NPA Ta Ƙara  Kaimi Wajen Janyo Masu Zuba Hannun Jari

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

Shugaban Kasar Sin Ya Jaddada Muhimmancin Samun Ci Gaba Mai Inganci Ta Fuskar Raya Wayewar Kai

May 23, 2025
Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

Ta Yaya Kasashe Masu Tasowa Za Su Iya Tinkarar Yakin Haraji Da Amurka Ta Tayar?

May 23, 2025
Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

May 23, 2025
Wasu ‘Yan Siyasa Da Jami’an Tsaro Na Taimaka Wa Boko Haram – Zulum

‘Yan Ta’adda Na Amfani Da Na’urorin Zamani Daidai Lokacin Da Sojoji Ke Da Karancin Makamai -Zulum

May 23, 2025
Dan Asalin Jihar Kano Ya Kafa Tarihin Kirkirar Manhaja Mai Auna Tsayin Bishiya A Faransa

Dan Asalin Jihar Kano Ya Kafa Tarihin Kirkirar Manhaja Mai Auna Tsayin Bishiya A Faransa

May 23, 2025
Tawagar FCT Na Ci Gaba da Lashe Lambobin Yabo a Gasar Wasanni Ta Ƙasa 

Tawagar FCT Na Ci Gaba da Lashe Lambobin Yabo a Gasar Wasanni Ta Ƙasa 

May 23, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jaridar Da Ya Fallasa ‘Sharrin’ Da Ake Shirya Wa Natasha

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jaridar Da Ya Fallasa ‘Sharrin’ Da Ake Shirya Wa Natasha

May 23, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Amince Da Lasisin Aikin Hakar Mai A Arewa

May 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram 16 A Borno Bayan Sun Kawo Hari Barikinsu

Sojoji Sun Kashe Ƴan Boko Haram 16 A Borno Bayan Sun Kawo Hari Barikinsu

May 23, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Zai Bibiyi Kwazon Ministocinsa A Ranar 29 Ga Watan Mayu

May 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.