• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Kasashen Afirka Da Na Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Nuna Alhinin Rasuwar Jiang Zemin

by CMG Hausa
3 years ago
Jiang Zemin

Shugabannin kasashen Afirka, da manyan jami’an kungiyoyin kasa da kasa, sun ci gaba da gabatar da sako zuwa ga shugaban kasar Sin Xi Jinping, inda suke nuna matukar alhini ga rasuwar Jiang Zemin.

A cikin sakon sa, shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya ce, marigayin ya jagoranci kasar Sin wajen aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje, da kama hanyar raya tattalin arziki yadda ya kamata, al’amarin da ya shaidawa duniya cewa, kasa za ta iya cimma burin raya tattalin arzikinta ta hanyar dogaro da kan ta. Buhari ya ce, nasarorin da marigayin ya samu a fannin tattalin arziki, suna da babban tasiri, wadanda ba za’a iya mantawa da su ba.

  • Shugabannin Kasashe Da Kungiyoyin Kasa Da Kasa Su Bayyana Jimamin Rasuwar Jiang Zemin

A nasa bangaren, shugaban kasar Kenya William Samoei Ruto, ya ce a matsayinsa na wani gogaggen jami’in siyasa, Jiang Zemin ya dukufa ka’in da na’in, wajen aza tubalin tattalin arziki mai inganci, da tabbatar da zaman lafiya a duniya. Shugaban ya gabatar da jaje ga iyalai, da abokansa, gami da daukacin al’ummar kasar Sin baki daya.

Shi ma shugaban kasar Senegal Macky Sall, ya bayyana matukar alhini ga rasuwar tsohon shugaba Jiang, da girmama manyan nasarorin da ya samu, tare kuma da jajantawa al’ummar kasar ta Sin.

Sai kuma shugaban hukumar zartaswar tarayyar Afirka AU, Moussa Faki Mahamat, cewa ya yi shugaba Jiang Zemin, fitacce ne a fagen siyasar kasar Sin da ta dukkanin duniya, kuma rasuwar sa, babban rashi ne ga kasar Sin, da ma aminanta a duniya. Faki ya tausayawa gwamnati, da jama’ar kasar Sin, gami da iyalan marigayin, a madadin hukumar zartaswar AU.

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Bugu da kari, jakadun wasu kasashen Afirka dake kasar Sin, ciki har da Najeriya, da Masar, da Aljeriya, da Mauritaniya, da Afirka ta Kudu, da Kamaru, da Senegal, su ma sun ziyarci ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, inda suka gabatar da matukar alhini ga rasuwar Jiang Zemin. (Murtala Zhang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
Next Post
An Gina Katafaren Masallacin Da Ya Fi Kowanne Girma A Duniya

An Gina Katafaren Masallacin Da Ya Fi Kowanne Girma A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

Shugaba Tinubu Da Shugaban Ƙasar Saliyo, Sun Yi Ganawar Sirri A Abuja

November 8, 2025
Majalisa Na Binciken Kwangilar Titin Naira Biliyan 1.46 Da Aka Yi Watsi Da Shi A Kaduna

Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna

November 8, 2025
Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

Majalisa Ta Ƙaryata Karɓar Dala Miliyan 10 Don Daƙile Tantance Shugaban NERC

November 8, 2025
An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.