ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin Kasashen Afirka Da Na Kungiyoyin Kasa Da Kasa Sun Nuna Alhinin Rasuwar Jiang Zemin

by CMG Hausa
3 years ago
Jiang Zemin

Shugabannin kasashen Afirka, da manyan jami’an kungiyoyin kasa da kasa, sun ci gaba da gabatar da sako zuwa ga shugaban kasar Sin Xi Jinping, inda suke nuna matukar alhini ga rasuwar Jiang Zemin.

A cikin sakon sa, shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya ce, marigayin ya jagoranci kasar Sin wajen aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje, da kama hanyar raya tattalin arziki yadda ya kamata, al’amarin da ya shaidawa duniya cewa, kasa za ta iya cimma burin raya tattalin arzikinta ta hanyar dogaro da kan ta. Buhari ya ce, nasarorin da marigayin ya samu a fannin tattalin arziki, suna da babban tasiri, wadanda ba za’a iya mantawa da su ba.

  • Shugabannin Kasashe Da Kungiyoyin Kasa Da Kasa Su Bayyana Jimamin Rasuwar Jiang Zemin

A nasa bangaren, shugaban kasar Kenya William Samoei Ruto, ya ce a matsayinsa na wani gogaggen jami’in siyasa, Jiang Zemin ya dukufa ka’in da na’in, wajen aza tubalin tattalin arziki mai inganci, da tabbatar da zaman lafiya a duniya. Shugaban ya gabatar da jaje ga iyalai, da abokansa, gami da daukacin al’ummar kasar Sin baki daya.

ADVERTISEMENT

Shi ma shugaban kasar Senegal Macky Sall, ya bayyana matukar alhini ga rasuwar tsohon shugaba Jiang, da girmama manyan nasarorin da ya samu, tare kuma da jajantawa al’ummar kasar ta Sin.

Sai kuma shugaban hukumar zartaswar tarayyar Afirka AU, Moussa Faki Mahamat, cewa ya yi shugaba Jiang Zemin, fitacce ne a fagen siyasar kasar Sin da ta dukkanin duniya, kuma rasuwar sa, babban rashi ne ga kasar Sin, da ma aminanta a duniya. Faki ya tausayawa gwamnati, da jama’ar kasar Sin, gami da iyalan marigayin, a madadin hukumar zartaswar AU.

LABARAI MASU NASABA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Bugu da kari, jakadun wasu kasashen Afirka dake kasar Sin, ciki har da Najeriya, da Masar, da Aljeriya, da Mauritaniya, da Afirka ta Kudu, da Kamaru, da Senegal, su ma sun ziyarci ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, inda suka gabatar da matukar alhini ga rasuwar Jiang Zemin. (Murtala Zhang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara
Daga Birnin Sin

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Next Post
An Gina Katafaren Masallacin Da Ya Fi Kowanne Girma A Duniya

An Gina Katafaren Masallacin Da Ya Fi Kowanne Girma A Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.