• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 month ago
PDP

Duk da irin mawuyacin hali da babbar jam’iyyar adawa ta PDP take ciki, kan babban taronta na kasa a watan Nuwamba na wannan shekara, wani sabon rudani ya kara turnuke shugabannin jam’iyyar adawa sakamakon yadda jam’iyya mai mulki ta APC take zawarcin wasu gwamnonin PDP.

 

Rahotanni na nuna cewa jam’iyyar PDP na dab da rasa wani gwamna daga yankin kudu, wanda aka bayyana cewa a yanzu haka ya kammala shirye-shiryen sauya sheka shi da magoya bayansa.

  • Kungiyar Masana’antu Ta Yi Fatali Da Sake Gabatar Da Haraji Na Kaso 4 Na Kwastom
  • Sin: Shawarar Gina Kyakkyawar Makomar Bil Adam Ta Bai Daya Ta Samu Amincewa A Duniya

Jam’iyyar PDP na fama da matsaloli masu yawa wanda har ta kai ga rasa gwamnoni biyu wadanda suka koma jam’iyyar APC a cikin watannin da suka gabata, amma jam’iyya na ci gaba da kare kanbunta, yayin da aka tabbatar da cewa Shugaba kasa Bola Tinubu idan ya dawo daga daga ziyarar kasashen waje zai karbi wani gwamna na PDP wanda zai sauya sheka daga PDP zuwa jam’iyyar APC.

 

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

“Zan iya tabbatar muku da cewa an kammala dukkan sharye-sherye na sauya shekan wani gwamna na PDP zuwa cikin APC. Ana ganin wannan gwamna a matsayin gwamna mai aiki tukuru da kwazo wanda yake da farin jini sosai a fagen siyasa a jiharsa. Abin da zan iya cewa a yanzu shi ne, ya kasance yana bangaren jihohin kuduncin Nijeriya ne. Mun gama dukan wasu shirye-shirye, muna jiran dawowar shugaban kasa daga kasashen waje don bayyana ficewarsa a hukumance,” in ji wata majiya.

 

Duk da cewa majiyar bai ambaci sunan gwamnan da abin ya shafa ba, idan zama a iya tunawa dai PDP tana da matukar karfi a bangaren siyasar kudancin Nijeriya. A kudu maso gabas, Gwamnan Jihar Inugu, Peter Mbah ne kawai daga jam’iyyar PDP, yayin da a kudu maso kudu a yanzu haka dai akwai gwamnan da aka dakatar Sim Fubara na Jihar Ribas da Gwamnan Jihar Bayelsa, Duoye Diri, yayin da kudu maso yamma ma tana da gwamnonin biyu ciki har da Seyi Makinde na Jihar Oyo da Ademola Adeleke na Jihar Osun.

 

APC za ta iya samun gagarumin rinjaye a jihohin kudu maso yamma idan Gwamna Mbah ya koma jam’iyyar, wanda shi ne kadai gwamnan PDP a wannan yanki, domin hakan zai daukaka yawan gwamnonin APC zuwa uku a wannan yanki. Haka nan lamarin zai iya faruwa a yankin kudu maso kudu idan Gwamna Fubara ko Gwamna Diri suka koma jam’iyyar APC daga jam’iyyar adawa ta PDP. Saboda haka, yawan gwamnonin a kudu maso kudu na iya karuwa daga biyar zuwa shida.

 

Majiyoyi da ke kusa da APC da PDP sun ce daya daga cikin gwamnonin PDP ya riga ya fice daga jam’iyyar PDP, kuma Shugaban kasa Tinubu zai karbi gwamnan zuwa APC lokacin da ya dawo daga tafiya.

 

Haka kuma majiya daga daya daga cikin gwamnonin yankin kudu ya tabbatar da cewa a daga cikin gwamnonin PDP na yankin kudu cewa ya riga ya fice daga PDP, kuma ko da yake gwamnan tun da farko yana son zama a cikin jam’iyyar don yin aiki tukuru wajen ganin an sake zaben Shugaban kasa Tinubu a 2027, an bayyana cewa ya dauki matakin barin PDP ya koma APC domin hakarsa ta cimma ruwa.

 

“Ya dai koma APC ne don samun nasarar ganin ya karfafa jam’iyyar a jihohin kudu da kuma samun karfi a arewa ta tsakiya da sauran yankunan Nijeriya gaban zaben 2027. Tuni dai mun karbi gwamnonin Delta da Akwa-Ibom a cikin jam’iyyar, kuma za mu ci gaba da amsar wasu a nan gaba,” in ji wata majiya.

 

An bayyana cewa sabon shirin da aka yi na ganin karin gwamnonin PDP sun fice zuwa jam’iyyar da ke mulki an kawo ta ne saboda abubuwan da ke faruwa a cikin jam’iyyar adawa ta ADC, inda aka fara samun labarai cewa jam’iyyar na iya amfani da tsarin karba-karba wajen fitar da dan takara a zaben 2027. An ruwaito cewa APC na shirin samun gagarumin nasara a kudu don rage tasirin da ake tunanin wani dan takara daga kudu zai iya yi, idan har dan takarar ADC ya fito daga wannan yankin.

 

Wata majiya ta ce, “Muna ganin cewa ADC na sake gabatar da wasu dubaru ta hanyoyi daban-daban. Idan wannan jam’iyyar ta tsayar da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar daga arewa maso gabas, hakan zai rage samun kuri’un kudancin kasar nan. Amma idan wannan jam’iyyar ta tsayar da wani dan takara daga kudu, hakan zai jawo hankalin shugaban da ke kan mulki, wanda zai bukaci ya tabbatar da karfin iko a wannan yanki. Wannan shi ne dalilin da ya sa jam’iyyar da kuma fadar shugaban kasar ba sa barin abubuwa su je ba tare da tsari ba ta hanyar mai da hankali kan zawarcin masu gwamnonin PDP masu tasiri.”

 

Kazalika, an bayyana cewa cikin gwamnonin da APC ke zawarci sun hada da Gwamnan Jihar Inugu, Peter Ndubuisi Mbah, Gwamnan Jihar Bayelsa, Douye Diri, Gwamnan Jihar Filato, Caleb Muftwang da Gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Dauda Lawal.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
Tambarin Dimokuradiyya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Tambarin Dimokuradiyya

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Next Post
Sin Ta Sanar Da Rukuni Na Hudu Na Abubuwa Da Wuraren Tunawa Da Yakin Kin Jinin Mamayar Dakarun Japan

Sin Ta Sanar Da Rukuni Na Hudu Na Abubuwa Da Wuraren Tunawa Da Yakin Kin Jinin Mamayar Dakarun Japan

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

Kasar Sin Ta Samu Manyan Nasarori A Fannin Inganta Walwalar Yara Da Tsoffi Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata  

October 10, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

2027: INEC Ta Nemi A Gaggauta Amincewa Da Ƙudirin Sake Fasalin Tsarin Zaɓe

October 10, 2025
Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

Sin Ta Gabatar Da Shawarwari Shida Game Da Karfafa Tsarin Shari’a Da Inganta Shugabanci A Duniya

October 10, 2025
Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya

October 10, 2025
Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.