• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
3 weeks ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da irin mawuyacin hali da babbar jam’iyyar adawa ta PDP take ciki, kan babban taronta na kasa a watan Nuwamba na wannan shekara, wani sabon rudani ya kara turnuke shugabannin jam’iyyar adawa sakamakon yadda jam’iyya mai mulki ta APC take zawarcin wasu gwamnonin PDP.

 

Rahotanni na nuna cewa jam’iyyar PDP na dab da rasa wani gwamna daga yankin kudu, wanda aka bayyana cewa a yanzu haka ya kammala shirye-shiryen sauya sheka shi da magoya bayansa.

  • Kungiyar Masana’antu Ta Yi Fatali Da Sake Gabatar Da Haraji Na Kaso 4 Na Kwastom
  • Sin: Shawarar Gina Kyakkyawar Makomar Bil Adam Ta Bai Daya Ta Samu Amincewa A Duniya

Jam’iyyar PDP na fama da matsaloli masu yawa wanda har ta kai ga rasa gwamnoni biyu wadanda suka koma jam’iyyar APC a cikin watannin da suka gabata, amma jam’iyya na ci gaba da kare kanbunta, yayin da aka tabbatar da cewa Shugaba kasa Bola Tinubu idan ya dawo daga daga ziyarar kasashen waje zai karbi wani gwamna na PDP wanda zai sauya sheka daga PDP zuwa jam’iyyar APC.

 

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

“Zan iya tabbatar muku da cewa an kammala dukkan sharye-sherye na sauya shekan wani gwamna na PDP zuwa cikin APC. Ana ganin wannan gwamna a matsayin gwamna mai aiki tukuru da kwazo wanda yake da farin jini sosai a fagen siyasa a jiharsa. Abin da zan iya cewa a yanzu shi ne, ya kasance yana bangaren jihohin kuduncin Nijeriya ne. Mun gama dukan wasu shirye-shirye, muna jiran dawowar shugaban kasa daga kasashen waje don bayyana ficewarsa a hukumance,” in ji wata majiya.

 

Duk da cewa majiyar bai ambaci sunan gwamnan da abin ya shafa ba, idan zama a iya tunawa dai PDP tana da matukar karfi a bangaren siyasar kudancin Nijeriya. A kudu maso gabas, Gwamnan Jihar Inugu, Peter Mbah ne kawai daga jam’iyyar PDP, yayin da a kudu maso kudu a yanzu haka dai akwai gwamnan da aka dakatar Sim Fubara na Jihar Ribas da Gwamnan Jihar Bayelsa, Duoye Diri, yayin da kudu maso yamma ma tana da gwamnonin biyu ciki har da Seyi Makinde na Jihar Oyo da Ademola Adeleke na Jihar Osun.

 

APC za ta iya samun gagarumin rinjaye a jihohin kudu maso yamma idan Gwamna Mbah ya koma jam’iyyar, wanda shi ne kadai gwamnan PDP a wannan yanki, domin hakan zai daukaka yawan gwamnonin APC zuwa uku a wannan yanki. Haka nan lamarin zai iya faruwa a yankin kudu maso kudu idan Gwamna Fubara ko Gwamna Diri suka koma jam’iyyar APC daga jam’iyyar adawa ta PDP. Saboda haka, yawan gwamnonin a kudu maso kudu na iya karuwa daga biyar zuwa shida.

 

Majiyoyi da ke kusa da APC da PDP sun ce daya daga cikin gwamnonin PDP ya riga ya fice daga jam’iyyar PDP, kuma Shugaban kasa Tinubu zai karbi gwamnan zuwa APC lokacin da ya dawo daga tafiya.

 

Haka kuma majiya daga daya daga cikin gwamnonin yankin kudu ya tabbatar da cewa a daga cikin gwamnonin PDP na yankin kudu cewa ya riga ya fice daga PDP, kuma ko da yake gwamnan tun da farko yana son zama a cikin jam’iyyar don yin aiki tukuru wajen ganin an sake zaben Shugaban kasa Tinubu a 2027, an bayyana cewa ya dauki matakin barin PDP ya koma APC domin hakarsa ta cimma ruwa.

 

“Ya dai koma APC ne don samun nasarar ganin ya karfafa jam’iyyar a jihohin kudu da kuma samun karfi a arewa ta tsakiya da sauran yankunan Nijeriya gaban zaben 2027. Tuni dai mun karbi gwamnonin Delta da Akwa-Ibom a cikin jam’iyyar, kuma za mu ci gaba da amsar wasu a nan gaba,” in ji wata majiya.

 

An bayyana cewa sabon shirin da aka yi na ganin karin gwamnonin PDP sun fice zuwa jam’iyyar da ke mulki an kawo ta ne saboda abubuwan da ke faruwa a cikin jam’iyyar adawa ta ADC, inda aka fara samun labarai cewa jam’iyyar na iya amfani da tsarin karba-karba wajen fitar da dan takara a zaben 2027. An ruwaito cewa APC na shirin samun gagarumin nasara a kudu don rage tasirin da ake tunanin wani dan takara daga kudu zai iya yi, idan har dan takarar ADC ya fito daga wannan yankin.

 

Wata majiya ta ce, “Muna ganin cewa ADC na sake gabatar da wasu dubaru ta hanyoyi daban-daban. Idan wannan jam’iyyar ta tsayar da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar daga arewa maso gabas, hakan zai rage samun kuri’un kudancin kasar nan. Amma idan wannan jam’iyyar ta tsayar da wani dan takara daga kudu, hakan zai jawo hankalin shugaban da ke kan mulki, wanda zai bukaci ya tabbatar da karfin iko a wannan yanki. Wannan shi ne dalilin da ya sa jam’iyyar da kuma fadar shugaban kasar ba sa barin abubuwa su je ba tare da tsari ba ta hanyar mai da hankali kan zawarcin masu gwamnonin PDP masu tasiri.”

 

Kazalika, an bayyana cewa cikin gwamnonin da APC ke zawarci sun hada da Gwamnan Jihar Inugu, Peter Ndubuisi Mbah, Gwamnan Jihar Bayelsa, Douye Diri, Gwamnan Jihar Filato, Caleb Muftwang da Gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Dauda Lawal.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Kasar Sin Sun Gudanar Da Hada-Hada Bisa Daidaito Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Nan

Next Post

Sin Ta Sanar Da Rukuni Na Hudu Na Abubuwa Da Wuraren Tunawa Da Yakin Kin Jinin Mamayar Dakarun Japan

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

4 weeks ago
Next Post
Sin Ta Sanar Da Rukuni Na Hudu Na Abubuwa Da Wuraren Tunawa Da Yakin Kin Jinin Mamayar Dakarun Japan

Sin Ta Sanar Da Rukuni Na Hudu Na Abubuwa Da Wuraren Tunawa Da Yakin Kin Jinin Mamayar Dakarun Japan

LABARAI MASU NASABA

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
PDP

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
PDP

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.