Wata tawaga mai girma daga jam’iyyar PDP karkashin jagorancin mukaddashin shugabanta na kasa, Ambasada Umar Damagum, ta kai ziyarar neman karin haske a hedikwatar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ke Abuja ranar Talata.
Kamar yadda INEC ta wallafa a shafinta na facebook, tawagar ta samu kyakkyawar tarba daga shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, tare da kwamishinoninta, manyan mataimaka, da kuma manyan daraktocin hukumar.
“Makasudin ziyarar a fili take: don tattaunawa da INEC kai tsaye kan matsalolin cikin gida da suka shafi jam’iyyar PDP, musamman ma wadanda ke bukatar tantance ka’idojin hukumar,” in ji INEC.
A jawabinsa na bude taron, Farfesa Yakubu ya jaddada aniyar INEC na gudanar da ayyukanta na doka, inda ya ce, “Aikinmu shi ne tabbatar da cewa an bi ka’ida.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp