• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

SIMDA Ta Ƙulla Alaƙa Da Jami’ar Skyline Kan Ci Gaban Ilimi Da Kasuwancin Zamani A Kano

by Muhammad
9 months ago
SIMDA

Gamayyar Kungiyar Ci gaban Kasuwar Singa da ke Kano a karkashin Jagorancin Shugaban ƙungiyar, Barista Junaidu Muhammad Zakari da Shugaban Dattijan Ƙungiyar kuma shugaban rukunonin Kamfanin Sambajo, Alhaji Salisu Sambajo, sun karɓi baƙuncin tawagar wakilan Jami’ar Skyline da ke Kano a ranar Alhamis 16, ga watan Janairun 2025 a ofishin Sambajo da ke Kasuwar Singa Kano.

Tawagar wakilan Jami’ar Skyline ta kawo ne ziyarar ne a ƙarƙashin jagorancin uban Jami’ar, Mista Nitin Anand da Daraktan Jami’ar, Abubakar Sadik Isma’il.

  • Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump
  • Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

Babbban makasudin kawo shi ne sanya albarka daga Shugaban Dattijan Kungiyar SIMDA, Alhaji Salisu Sambajo da ƙulla alaƙa mai ƙarfi da ƙungiyar SIMDA kan bunkasa harkokin kasuwanci da ilimi a jihar Kano.

A jawabin Mista Anand na Jami’ar Skyline ya ce, su na neman tabarrakin Alhaji Salisu Sambajo da ƙungiyar SIMDA da kuma neman ta su gudunmawar wajen bunkasa harkokin Jami’ar da ɓangaren ilimi da kasuwanci a Kano.

Ya kuma yi alkawarin bai wa shugabancin ƙungiyar SIMDA ragin kuɗaɗen shiga makarantar da kashi 50 cikin kashi 100 kan duk ɗalibin da Kungiyar ta dauki nauyin bai wa tallafin karatu a jami’ar, sannan Jami’ar za ta bai wa mambobin Kasuwar Singa bita da horo na yini guda kyauta da kuma ba su takardar shaidar horo a kan kasuwancin zamani a matsayin wani bangare na tukuici ga ƙungiyar ta SIMDA.

LABARAI MASU NASABA

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

A jawabin dattijon Ƙungiyar SIMDA kuma shugaban rukunonin Kamfanin Sambajo, Alhaji Salisu Sambajo, ya bayyana farin cikinsa da jin daɗi kan kawo ziyarar wakilan Jami’ar, ya kuma yi alƙawarin bayar da duk wata gudunmowa da za ta kyautata alaƙa kan ci gaban ilimi da kasuwanci a tsakanin ƙungiyar SIMDA da Jami’ar.

Shugaban Ƙungiyar, Barista Junaidu Muhammad Zakari, ya gode wa wakilan Jami’ar bisa karrama su da su ka yi wajen kawo ziyarar, ya kuma ce su ma za su kai musu makamanciyar ziyarar don kara karfafa zumunci da tattaunawa kan yadda za a bunƙasa ɓangaren ilimi da kasuwanci a kasuwar.

Barista Junaidu ya ce, za su duba hanyoyin da za su bi don bayar da ta su gudunmawar a ƙungiyance.

Shugaban ya kuma gode wa Jami’ar kan horo da bitar da Jami’ar za ta shirya wa mambobin ƙungiyar na kasuwar Singa.

Taron ya samu halartar wasu daga cikin shugabanin ƙungiyar da mambobinta da sauransu.

SIMDA

SIMDA SIMDA SIMDA

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba
Manyan Labarai

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa
Ra'ayi Riga

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC
Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
Next Post
2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan 'Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

LABARAI MASU NASABA

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

Babu Rikici A Jam’iyyar APC A Nasarawa — Shugaban Jam’iyya

October 21, 2025
An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

An Ɗage Shari’ar Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Zuwa 19 Ga Watan Nuwamba

October 21, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 21, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

Mutane 3,433 Sun Rasu a Hatsarin Mota 6,858 Cikin Wata 9 A Nijeriya – FRSC

October 21, 2025
NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

NLC Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Don Biyan Buƙatun ASUU Da Sauran Ƙungiyoyi 

October 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Ɗan Fashi Sanye Da Kayan NYSC A Enugu

October 21, 2025
Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

Gwamnatin Gombe Ta Ceto Yara 59 Da Aka Yi Safararsu

October 21, 2025
Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.