ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

by Khalid Idris Doya
1 year ago
Fargaba

Kwanaki kalilan da shiga sabuwar shekarar 2025, sabbin hare-haren ‘yan ta’adda, ‘yan fashin daji da sauran ayyukan ta’addanci ya zama wani abu na tura razani a zukatan al’umma a sassa daban-daban na kasar nan.

A cewar rahotanni, sama da mutum 78 ne aka kashe, yayin da kuma aka yi garkuwa da wasu mutum 80 a sassan jihohi daban-daban a mako na farko na watan Janairun 2025.

  • Ranar Tunawa Da Mazan Jiya: Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Inganta Rayuwar Iyalan Jaruman Da Suka Rasu
  • Hauhawar Farashin Kayayyaki Ya Kai Kashi 34.80 A Disamban 2024 – NBS

A ranar Asabar 4 ga Janairu, kusan sojoji takwas aka kashe a lokacin da ‘yan ta’adda suka kai hari a sansanin sojoji da ke Sabon Gari a karamar hukumar Dambo ta Jihar Borno.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Argungu da ke Jihar Kebbi, inda suka kashe mutum biyu, lamarin da kakakin ‘yansandan Jihar Kebbi, Nafiu Abubakar ya tabbatar da faruwarsa.

Wani karin abun takaici shi ne, yadda aka samun labarin kai hari a Charanci, Safana, Kurfi, da karamar hukumar Kaita a jihar Katsina, inda aka kashe sama da mutum 30 a tsakanin ranar Talata zuwa Alhamis.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

An labarto cewa ‘yan bindiga ne suka farmaki mutanen a lokacin da suke dawowa daga ta’aziyya a karamar hukumar Batsari.

Haka kuma, ‘yan fashin daji sun kaddamar da munanan hare-hare a Jihar Borno da Kebbi, sannan wasu ‘yan bindiga da ba gano su waye ba da ke sheke ayarsu a yankin Umuokanne da ke Jihar Imo sun kashe mutane uku.

‘Yan awannin da harin Umuokanne, wasu ‘yan bindiga sun kaddamar da wani mummunar hari a Orsu ta Jihar Imo, inda mutum 18 suka rasa rayukansu.

A wani labarin kuma, wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan kungiyar ta’addan Lakurawa ne sun kashe ma’aikatan kamfanin Airtel guda biyu da wani mazaunin kauyen Gumki da ke karamar hukumar Arewa ta Jihar Kebbi a karshen mako.

An tattaro cewa ‘yan ta’addan sun mamaye al’ummar da ke tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar, bayan da suka samu labarin cewa kamfanin sadarwa na kafa wata kafa ta sa ido a yankin.

Wasu mutane 11 kuma aka kashe a kauyen Gululu da ke Jahun da Miga. Sannan a ranar Laraba 8 ga Janairu, ‘yan bindiga sun mamaye kauyen Idu da ke gundumar Kufana a karamar hukumar Kajuru tare da kashe mutum 2. A kuma wannan ranar an kashe jami’ai guda 2 a wani harin da ‘yan Boko Haram suka kai a caji ofis din ‘yansanda da ke Borno.

Haka zalika, an ruwaito cewa wasu ‘yan bindiga sun kashe wani manomi mai suna Terzungwe Shaku a kauyen Akor da ke karamar hukumar Guma a Jihar Benuwai.

Shaku, wanda kuma ya mallaki wurin shan giya a kasuwar Akor, an sace shi ne jim kadan kafin sabuwar shekara kuma aka yi garkuwa da shi sama da makonni biyu kafin a kashe shi.

Mazauna yankin sun ce da farko masu garkuwa da mutanen sun bukaci naira miliyan 20, amma dangin sun tattauna kan naira miliyan 5.4, inda suka amince kuma iyalan suka biya.

Mutane da dama ne suka biya kudin fansa domin ceto ‘yan uwansu daga garkuwar da ‘yan bindiga suka yi wa ‘yan uwansu.

Fargaba
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Lokacin Ya Yi Na Fahimtar Ainihin Kasar Sin

Lokacin Ya Yi Na Fahimtar Ainihin Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.