ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

SIMDA Ta Ƙulla Alaƙa Da Jami’ar Skyline Kan Ci Gaban Ilimi Da Kasuwancin Zamani A Kano

by Muhammad
1 year ago
SIMDA

Gamayyar Kungiyar Ci gaban Kasuwar Singa da ke Kano a karkashin Jagorancin Shugaban ƙungiyar, Barista Junaidu Muhammad Zakari da Shugaban Dattijan Ƙungiyar kuma shugaban rukunonin Kamfanin Sambajo, Alhaji Salisu Sambajo, sun karɓi baƙuncin tawagar wakilan Jami’ar Skyline da ke Kano a ranar Alhamis 16, ga watan Janairun 2025 a ofishin Sambajo da ke Kasuwar Singa Kano.

Tawagar wakilan Jami’ar Skyline ta kawo ne ziyarar ne a ƙarƙashin jagorancin uban Jami’ar, Mista Nitin Anand da Daraktan Jami’ar, Abubakar Sadik Isma’il.

  • Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump
  • Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

Babbban makasudin kawo shi ne sanya albarka daga Shugaban Dattijan Kungiyar SIMDA, Alhaji Salisu Sambajo da ƙulla alaƙa mai ƙarfi da ƙungiyar SIMDA kan bunkasa harkokin kasuwanci da ilimi a jihar Kano.

ADVERTISEMENT

A jawabin Mista Anand na Jami’ar Skyline ya ce, su na neman tabarrakin Alhaji Salisu Sambajo da ƙungiyar SIMDA da kuma neman ta su gudunmawar wajen bunkasa harkokin Jami’ar da ɓangaren ilimi da kasuwanci a Kano.

Ya kuma yi alkawarin bai wa shugabancin ƙungiyar SIMDA ragin kuɗaɗen shiga makarantar da kashi 50 cikin kashi 100 kan duk ɗalibin da Kungiyar ta dauki nauyin bai wa tallafin karatu a jami’ar, sannan Jami’ar za ta bai wa mambobin Kasuwar Singa bita da horo na yini guda kyauta da kuma ba su takardar shaidar horo a kan kasuwancin zamani a matsayin wani bangare na tukuici ga ƙungiyar ta SIMDA.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

A jawabin dattijon Ƙungiyar SIMDA kuma shugaban rukunonin Kamfanin Sambajo, Alhaji Salisu Sambajo, ya bayyana farin cikinsa da jin daɗi kan kawo ziyarar wakilan Jami’ar, ya kuma yi alƙawarin bayar da duk wata gudunmowa da za ta kyautata alaƙa kan ci gaban ilimi da kasuwanci a tsakanin ƙungiyar SIMDA da Jami’ar.

Shugaban Ƙungiyar, Barista Junaidu Muhammad Zakari, ya gode wa wakilan Jami’ar bisa karrama su da su ka yi wajen kawo ziyarar, ya kuma ce su ma za su kai musu makamanciyar ziyarar don kara karfafa zumunci da tattaunawa kan yadda za a bunƙasa ɓangaren ilimi da kasuwanci a kasuwar.

Barista Junaidu ya ce, za su duba hanyoyin da za su bi don bayar da ta su gudunmawar a ƙungiyance.

Shugaban ya kuma gode wa Jami’ar kan horo da bitar da Jami’ar za ta shirya wa mambobin ƙungiyar na kasuwar Singa.

Taron ya samu halartar wasu daga cikin shugabanin ƙungiyar da mambobinta da sauransu.

SIMDA

SIMDA SIMDA SIMDA

SIMDA
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Next Post
2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan 'Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.