• English
  • Business News
Saturday, June 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

SIMDA Ta Ƙulla Alaƙa Da Jami’ar Skyline Kan Ci Gaban Ilimi Da Kasuwancin Zamani A Kano

by Muhammad
5 months ago
in Labarai
0
SIMDA Ta Ƙulla Alaƙa Da Jami’ar Skyline Kan Ci Gaban Ilimi Da Kasuwancin Zamani A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gamayyar Kungiyar Ci gaban Kasuwar Singa da ke Kano a karkashin Jagorancin Shugaban ƙungiyar, Barista Junaidu Muhammad Zakari da Shugaban Dattijan Ƙungiyar kuma shugaban rukunonin Kamfanin Sambajo, Alhaji Salisu Sambajo, sun karɓi baƙuncin tawagar wakilan Jami’ar Skyline da ke Kano a ranar Alhamis 16, ga watan Janairun 2025 a ofishin Sambajo da ke Kasuwar Singa Kano.

Tawagar wakilan Jami’ar Skyline ta kawo ne ziyarar ne a ƙarƙashin jagorancin uban Jami’ar, Mista Nitin Anand da Daraktan Jami’ar, Abubakar Sadik Isma’il.

  • Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump
  • Za A Kammala Aikin Titin Abuja-Kaduna-Kano Cikin Watanni 14 – Gwamnati

Babbban makasudin kawo shi ne sanya albarka daga Shugaban Dattijan Kungiyar SIMDA, Alhaji Salisu Sambajo da ƙulla alaƙa mai ƙarfi da ƙungiyar SIMDA kan bunkasa harkokin kasuwanci da ilimi a jihar Kano.

A jawabin Mista Anand na Jami’ar Skyline ya ce, su na neman tabarrakin Alhaji Salisu Sambajo da ƙungiyar SIMDA da kuma neman ta su gudunmawar wajen bunkasa harkokin Jami’ar da ɓangaren ilimi da kasuwanci a Kano.

Ya kuma yi alkawarin bai wa shugabancin ƙungiyar SIMDA ragin kuɗaɗen shiga makarantar da kashi 50 cikin kashi 100 kan duk ɗalibin da Kungiyar ta dauki nauyin bai wa tallafin karatu a jami’ar, sannan Jami’ar za ta bai wa mambobin Kasuwar Singa bita da horo na yini guda kyauta da kuma ba su takardar shaidar horo a kan kasuwancin zamani a matsayin wani bangare na tukuici ga ƙungiyar ta SIMDA.

Labarai Masu Nasaba

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

A jawabin dattijon Ƙungiyar SIMDA kuma shugaban rukunonin Kamfanin Sambajo, Alhaji Salisu Sambajo, ya bayyana farin cikinsa da jin daɗi kan kawo ziyarar wakilan Jami’ar, ya kuma yi alƙawarin bayar da duk wata gudunmowa da za ta kyautata alaƙa kan ci gaban ilimi da kasuwanci a tsakanin ƙungiyar SIMDA da Jami’ar.

Shugaban Ƙungiyar, Barista Junaidu Muhammad Zakari, ya gode wa wakilan Jami’ar bisa karrama su da su ka yi wajen kawo ziyarar, ya kuma ce su ma za su kai musu makamanciyar ziyarar don kara karfafa zumunci da tattaunawa kan yadda za a bunƙasa ɓangaren ilimi da kasuwanci a kasuwar.

Barista Junaidu ya ce, za su duba hanyoyin da za su bi don bayar da ta su gudunmawar a ƙungiyance.

Shugaban ya kuma gode wa Jami’ar kan horo da bitar da Jami’ar za ta shirya wa mambobin ƙungiyar na kasuwar Singa.

Taron ya samu halartar wasu daga cikin shugabanin ƙungiyar da mambobinta da sauransu.

SIMDA

SIMDA SIMDA SIMDA


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ƊalibaiJami'akanoƘungiyaSinga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilin Musamman Na Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Rantsar Da Donald Trump

Next Post

2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

Related

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako
Labarai

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

56 minutes ago
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80
Labarai

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

3 hours ago
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5
Manyan Labarai

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

8 hours ago
Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Matafiya 12 A Filato 

9 hours ago
Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya
Labaran Kasuwanci

Kuratan Sojoji 1,196 Aka Yaye A Makarantar Horar Da Sojoji Ta Zariya

10 hours ago
Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa
Labarai

Minista Ya Yaba Wa Hafsoshin Soji Kan Cigaban Da Aka Samu A Fannin Tsaron Ƙasa

11 hours ago
Next Post
2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan ‘Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

2025: Fargaba Na Kara Mamaye Zukatan 'Yan Nijeriya Kan Yadda Ake Samun Garkuwa Da Mutane

LABARAI MASU NASABA

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

June 21, 2025
CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

CMG Ya Ja Hankulan Baki A Dandalin Tattaunawar Tattalin Arziki Na Kasa Da Kasa Na St. Petersburg Karo Na 28 

June 21, 2025
Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

Yankin Taiwan Ya Yi Taron Bikin Bauta Na Kakan Gargajiyar Sin Fuxi

June 21, 2025
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

June 21, 2025
Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Rasha Don Daukaka Amincewar Juna Ta Fuskar Siyasa Da Karfafa Muradun Juna

June 21, 2025
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

June 21, 2025
Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

Tottenham Da West Ham Sun Nuna Sha’awar Daukar Dan Wasan Nijeriya Raphael Onyedika

June 21, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

Wakilin Sin Ya Yi Kira A Yayyafa Ruwa Ga Rikicin Isra’ila Da Iran

June 21, 2025
Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

Kungiyar Gamayyar Gidajen Rediyo Da Telabijin Na Kasashen Afirka Ta Ba CMG Kyautar Karramawa

June 21, 2025
Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

Bam Ya Fashe A Kano, Ya Kashe Mutane 5

June 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.