• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Afirka Za Su Ci Gaba Da Aiwatar Da Tsare-tsaren Ayyukan Hadin Gwiwa 10 

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
Sin

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana a jiya Juma’a cewa, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka wajen samar da sakamako masu inganci daga tsaren-tsaren ayyukan hadin gwiwa 10 da aka gabatar a taron kolin dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) da aka gudanar a birnin Beijing a shekarar da ta gabata, tare da tabbatar da cewa, bangarorin biyu sun samu ci gaba kan hanyar zamanantarwa cikin sauri, da kwanciyar hankali.

Wang ya bayyana hakan ne a wata hirar da ya yi da kafafen yada labarai na kasar Sin bayan ziyarar da ya kai kasashen Namibia, Jamhuriyar Kongo, Chadi da Najeriya.

  • Kasuwar ‘Yan Wasa: Omar Marmoush Na Dab Da Komawa Manchester City
  • Za Mu Tabbatar Da Samun Kyakkyawar Alaka Da Gwamnati Don Ci Gaban Kasuwar Kofar Ruwa – ‘Yanleman

Wang ya kara da cewa, shugaban Jamhuriyar Kongo Denis Sassou Nguesso da wasu shugabannin kasashen Afirka sun bayyana cewa, tsare-tsaren ayyukan hadin gwiwa guda 10, sun shafi dukkan fannoni na hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, da tinkarar kalubalen da Afirka ke fuskanta, da daidaita bukatun Afirka, kuma za su ba da goyon baya mai yawa ga ci gaba da farfadowar nahiyar ta Afirka.

Kazalika, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da kasashen Afirka wajen sa kaimi ga gudanar da harkokin daidaita sauyin yanayi a duniya, da kiyaye ka’idar “ana tare a zahiri amma an sha bamban a daukar alhaki”, kana ta bukaci kasashe masu ci gaba da su amince da nauyin da ke wuyansu na tarihi, da kuma sauke nauyin da aka rataya a wuyansu, da ba da tallafi na kudi, fasaha, da kara sanin makamar aiki ga kasashe masu tasowa, musamman ma kasashen Afirka.

A hadin gwiwa a fannin aikin gona kuwa, ministan harkokin wajen kasar Sin ya bayyana wasu muhimman fannoni guda biyar da kasar Sin za ta mai da hankali a kai, wadanda suka hada da samar da abinci, da rage fatara, da kara sanin makamar aiki, da saukaka harkokin kasuwanci, da sada zumunta, domin gaggauta aiwatar da sakamakon taron kolin FOCAC na Beijing a fannin aikin gona.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

Da yake karin haske game da yadda kasashe masu tasowa ke samun ci gaba duk da sauye-sauyen da duniya ke fuskanta, Wang ya ce, Sin da Afirka su ne ginshikann ci gaba da farfado da kasashe masu tasowa na duniya, kuma suna da ra’ayin gina tsarin tafiyar da harkokin duniya mai adalci da daidaici.

Wang ya ci gada da cewa, a matsayinta na muhimmiyar aminiya kuma abokiyar huldar Afirka, kasar Sin za ta ci gaba da ba da goyon baya ga kasashen Afirka ba tare da kakkautawa ba, wajen gyara zaluncin da aka yi musu a tarihi, da yin kakkausar suka ga duk wani tsoma bakin waje a harkokin cikin gidan Afirka, tare da ba da shawarar samar da shirye-shirye na musamman don tinkarar matsalolin Afirka wajen yin kwaskwarima ga kwamitin sulhu na MDD. (Mohammed Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025
Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Ta Saka Burikan Da Za Ta Cika A Shekaru 5 Masu Zuwa

October 24, 2025
Next Post
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kawo Moriya Ga Bunkasar Masar

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ta Kawo Moriya Ga Bunkasar Masar

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

October 25, 2025
Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025
Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

Ba Zan Kwatanta Matsayina Da Na Sarkin Bauchi Ba – Sabon Sarkin Duguri

October 24, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

Gwamnatin Kaduna Ta Gano Ma’adanin Zinari Da Tagulla Da Za Su Haɓaka Tattalin Arziƙin Jihar

October 24, 2025
An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Kebe Ranar 25 Ga Oktoba A Matsayin Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.